< 1 Krønikebok 15 >
1 Siden bygget han sig huser i Davids stad og gjorde i stand et sted for Guds ark og reiste et telt for den.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Da sa David: Ingen skal bære Guds ark uten levittene; for dem har Herren utvalgt til å bære Guds ark og til å tjene ham for alle tider.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 Så samlet David hele Israel til Jerusalem for å føre Herrens ark op til det sted som han hadde gjort i stand for den.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 Og David kalte Arons barn og levittene sammen:
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 av Kahats barn Uriel, den øverste, og hans brødre, hundre og tyve,
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 av Meraris barn Asaja, den øverste, og hans brødre, to hundre og tyve,
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 av Gersoms barn Joel, den øverste, og hans brødre, hundre og tretti,
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 av Elisafans barn Semaja, den øverste, og hans brødre, to hundre,
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 av Hebrons barn Eliel, den øverste, og hans brødre, åtti.
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 av Ussiels barn Amminadab, den øverste, og hans brødre, hundre og tolv.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 Så kalte David til sig prestene Sadok og Ebjatar og levittene Uriel, Asaja og Joel, Semaja og Eliel og Amminadab.
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 Og han sa til dem: I familiehoder for levittene, hellige eder, både I og eders brødre, og før Herrens, Israels Guds ark op til det sted jeg har gjort i stand for den!
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 Det var fordi I ikke var med første gang at Herren vår Gud brøt inn iblandt oss; for vi søkte ham ikke på rette måte.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 Da helliget prestene og levittene sig for å føre Herrens. Israels Guds ark op.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 Og levittenes barn bar Guds ark på sine skuldrer ved hjelp av bærestengene, således som Moses hadde påbudt efter Herrens ord.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 Så bød David de øverste blandt levittene at de skulde stille sine brødre sangerne frem med musikkinstrumenter, harper og citarer og cymbler, som de skulde spille på, idet de lot gledesangen tone.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 Da stilte levittene frem Heman, sønn av Joel, og av hans brødre Asaf, sønn av Berekja, og av deres brødre Meraris barn Etan, sønn av Kusaja,
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 og sammen med dem deres brødre av annen rang, Sakarja, Ben og Ja'asiel og Semiramot og Jehiel og Unni, Eliab og Benaja og Ma'aseja og Mattitja og Eliflehu og Mikneja og Obed-Edom og Je'iel, dørvokterne.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 Sangerne Heman, Asaf og Etan skulde slå på kobbercymbler;
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 Sakarja og Asiel og Semiramot og Jehiel og Unni og Eliab og Ma'aseja og Benaja skulde spille på harper efter Alamot,
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 og Mattitja og Eliflehu og Mikneja og Obed-Edom og Je'iel og Asasja på citarer efter Sjeminit for å lede sangen.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 Kenanja, levittenes sangmester, underviste i sangen; for han var kyndig i det.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 Berekja og Elkana var dørvoktere ved arken.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 Prestene Sebaina og Josafat og Netanel og Amasai og Sakarja og Benaja og Elieser blåste i trompeter foran Guds ark, og Obed-Edom og Jehia var dørvoktere ved arken.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 Så gikk David og Israels eldste og høvedsmennene over tusen avsted for å hente Herrens pakts-ark op fra Obed-Edoms hus under jubel.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 Og da nu Gud hjalp levittene som bar Herrens pakts-ark, ofret de syv okser og syv værer.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 David var klædd i en kåpe av hvitt bomullstøi, og likeså alle de levitter som bar arken, og sangerne og Kenanja, sangmesteren, som ledet sangen; dessuten hadde David en livkjortel av lerret på.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 Og hele Israel førte Herrens pakts-ark op med fryderop og med basunklang og med trompeter og cymbler, under harpe- og citarspill.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 Men da Herrens pakts-ark kom inn i Davids stad, da så Mikal, Sauls datter, ut gjennem vinduet, og hun så kong David hoppe og danse, og hun foraktet ham i sitt hjerte.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.