< Yohani 21 >

1 Pagamaliki genago, Yesu akavahumila kavili vawuliwa vaki pamuhana ya nyanja Tibelia. Avahumili naha,
Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa:
2 Simoni Petili, Tomasi mweikemewa Mapaha, na Natanyeli mkolonjinji wa Kana ya ku Galilaya, vana vavili va Zebedayo na vawuliwa vaki vangi vavili, vakavya voha pamonga.
Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu.
3 Simoni Petili akavajovela, “Nihamba kulova somba.” Vene vakamjovela, “Tete tilongosana na veve.” Vakahamba, vakakwela muwatu, nambu kilu yila nakupata chindu.
Saminu Bitrus yace masu, “Zani su.” sukace masa “Mu ma za mu je tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.
4 Hamba kucha, Yesu ayimili kumwambu ya nyanja, nambu vawuliwa vamanyili lepi kuvya avi Yesu.
To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane.
5 Yesu akavakota, “Vankozi, mupatili lepi somba?” Vakamyangula, “Lepi! Kawaka.”
Sai Yesu yace masu, “Samari, kuna da wani abinda za a ci?” Suka amsa masa sukace “A'a”.
6 Yesu akavajovela, “Muhelesa ngwanda upandi wa kulyela wa watu na nyenye yati mwipata somba.” Ndi vakazihelesa ngwanda, nambu hinu nakuhotola kuhuta kavili ndava ya somba zamahele.
Yace masu, “Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu.” Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
7 Kangi muwuliwa yula, Yesu mweamganili neju, akamjovela Petili, “Ndi Bambu!” Simoni Petili peayuwini kuvya ndi Bambu, akajikunga nyula yaki ya kuvala muni ahulili, akajitaga mumanji.
Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun.
8 Nambu vawuliwa vangi vala vabwelili kumbwani na watu kuni vihuta ngwanda zezimemili somba, vavi lepi kutali na pandumba, ndi vavi utali wa mita miya yimonga kuhuma mu mkingisa.
Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi.
9 Pavahikili pandumba wauwene motu wa makalakala, wiyaka, na panani yaki pavikiwi somba na libumunda.
Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
10 Yesu akavajovela, “Mgava somba zingi mleta penapa zemlovili.”
Yesu ya ce masu “Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu”.
11 Simoni Petili akayingila muwatu, akahuta mbaka kundumba ngwanda yila yeyimemili somba zivaha miya yimonga na makumi mhanu na zidatu. Pamonga wamemili somba zamahele, nambu ngwanda yadawiki lepi.
Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
12 Yesu akavajovela “Mbwela mlawuka.” Kawaka hati mmonga wavi. Mwealingili kumkota. “Veve ndi wayani,” Vammanyili kuvya Bambu.
Yesu yace masu, “Ku zo ku karya kumallo”. Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa “Ko shi wanene?” Domin sunsani Ubangiji ne.
13 Yesu akabwela, akatola, libumunda akavapela, akakita mewawa na somba zila.
Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin.
14 Yeniyi yavi mala ya datu Yesu kuvahumila vawuliwa vaki peamali kuyuka.
Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
15 Pevamali kulya, Yesu akamkota Simoni Petili, “Simoni mwana wa Yohani! Wu, ukunigana nene kuliku ava?” Mwene akayangula, “Ena, Bambu, umanyili kuvya nene nikukugana.” Yesu akamjovela, “Dima vana mambelele vangu.”
Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, “Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?” Bitrus yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka” Yesu yace masa “Ka ciyar da 'ya'yan tumakina”.
16 Kavili akamjovela, “Simoni mwana wa Yohani! Wu, ukunigana?” Petili akamyangula, “Ena, Bambu, umanyili kuvya nikukugana.” Yesu akamjovela “Dima mambelele gangu.”
Ya sake fada masa karo na biyu, “Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?” Bitrus Yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka”. Yesu yace masa, “Ka lura da Tumakina”.
17 Yesu akamkota mala ya datu, “Simoni mwana wa Yohani! Wu, ukunigana?” Penapo Petili akavya ngolongondi ndava amkotili mala ya datu. “Ukunigana?” Akamjovela, “Bambu, wamwene umanyili kila chindu, umanyili kuvya nene nikukugana.” Yesu akamjovela, “Dima mambelele gangu!
Ya sake fada masa, karo na uku, “Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, “Kana kaunata” Yace masa, “Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka.” Yesu yace masa “Ka ciyar da tumaki na.
18 Chakaka nikukujovela, pawavi msongolo wayovalili kujitendelekeha wamwene na kuhamba kwewigana. Nambu pawivya mgogolo wiyinula mawoko gaku, mundu yungi ndi yati akukunga na kuhamba kwe wangagana kuhamba.”
Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba.”
19 Yesu ajovili genago, kulangisa namuna Petili cheifwa na kumpela ukulu Chapanga. Kangi akamjovela Petili, “Nilanda.”
To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
20 Petili akang'anamuka, amuwene muwuliwa yula mweaganiwi na Yesu, akumlanda mweneuyo ndi yula mweatamili papipi neju na Yesu lukumbi pevalyayi na kumkota, “Bambu ndi yani mweakukung'anamukila?”
Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace “Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?”
21 Hinu, Petili peamuwene mwenuyo, akamkota Yesu, “Bambu, mundu uyu chikumuhumila kyani?”
Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu “Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?”
22 Yesu akayangula, “Ngati nigana asigalila mbaka penibwela, chikuvala kyani? Veve unilanda nene.”
Yesu yace masa, “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni.”
23 Malovi ago, gadandasiki pagati ya valongo vevakumsadika Kilisitu kuvya muwuliwa mwenuyo yati ifwa lepi. Nambu Yesu amjovili lepi muwuliwa yula ifwa lepi, nambu ajovili, “Ngati nigana asigalila mbaka panibwela yikukuvala kyani?”
Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?”
24 Mwenuyu ndi muwuliwa, mwealoli mambu ago na kugayandika. Tete timanyili ajovili chakaka.
Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne.
25 Gavi mambu gangi gamahele geagahengili Yesu. Ngati goha ngagiyandikwayi, niholela hati mulima woha nakuvya pandu pa kuvika hitabu yeyiyandikwi. Ena.
Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.

< Yohani 21 >