< 1 Yohani 5 >

1 Kila mundu mwaisadika kuvya Yesu ndi Kilisitu Msangula mundu mwenuyo ndi mwana wa Chapanga. Na kila mweakumugana dadi mewawa akumgana na mwana waki.
Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
2 Lijambu lenili ndi likutikita timanyayi kuvya tivaganili vana va Chapanga, ndi patikumugana Chapanga na kuyidakila mihilu yaki.
Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
3 Ndava kumugana Chapanga ndi kuyidakila mihilu yaki. Na mihilu yaki yitopa lepi,
Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
4 ndava kila mundu mweavi mwana wa Chapanga ihotola kugahotola mambu ga mulima uwu. Na tete tikuuhotola mulima kwa sadika yitu.
domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
5 Yani ihotola kugahotola mambu ga mulima? Ndi yula mweisadika kuvya Yesu ndi Mwana wa Chapanga.
Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
6 Yesu Kilisitu ndi mweabwelili kwa njila ya manji lukumbi lwa ubatizu na kwa ngasi peafwili. Abwelili lepi kwa njila ya manji ndu, nambu kwa manji na ngasi. Na Mpungu Msopi ijova aga ndi chakaka ndava ya Yesu muni Mpungu Msopi ndi mchakaka.
Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
7 Hinu vavi vadatu vevijova uchakaka.
Akwai shaidu uku, wato,
8 Mpungu Msopi, manji na ngasi, na voha viyidakilana chindu chimonga.
Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
9 Tete tisadika lukumbi vandu vakutijovela gavagaweni ndi gala geijova Chapanga gitopa neju na Chapanga ijova chakaka kumvala Mwana waki.
Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
10 Ndi kila mundu mweakumusadika mwana wa Chapanga avinawu wenuwo uchakaka mumtima waki. Nambu mweangamsadika Chapanga akumukita Chapanga kuvya mdese, ndava asadiki lepi mambu geajovili Chapanga kumvala Mwana waki.
Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
11 Na uchakaka wene ndi uwu: Chapanga atipelili wumi wa magono goha gangali mwishu, na wumi wenuwo upatikana kwa Mwana waki. (aiōnios g166)
Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios g166)
12 Mundu yoyoha mweavili na Mwana wa Chapanga avi na wumi wenuwo, na mundu mweavi lepi na Mwana wa Chapanga avi lepi na wumi wenuwo.
Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
13 Nivayandikili nambu mumanyayi kuvya muvinau wumi wa magono goha gangali mwishu, nyenye mwamukumsadiki Mwana wa Chapanga. (aiōnios g166)
Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios g166)
14 Lijambu lenili ndi likutikita timanya changali kuyogopa kuvya Chapanga akutiyuwanila, na tikamyupa chindu chochoha ngati cheigana akutiyuwana.
Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
15 Na tete tikamanyayi kuvya kila petiyupa akutiyuwana, ndi timanyi kuvya tipokela chochoha chatiyupa kwaki.
In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
16 Ngati mundu yati akamlola mlongo waki ikita gakumbudila Chapanga gangamlongosa mulifwa, iganikiwa amyupilayi, na Chapanga yati akumupela wumi mundu mwenuyo, nilongela aga ndava ya vala vavihenga uhakau wangavalongosa mulifwa. Nambu kuvili kumbudila Chapanga kwekumlongosa mundu mulifwa nene nijova lepi myupa ndava ya kumbudila Chapanga kwenuko.
Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
17 Lijambu loloha langamganisa Chapanga, lenilo ndi lijambu la kumbudila Chapanga, nambu kuvili kumbudila Chapanga kwanga mlongosa mundu mulifwa.
Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
18 Timanyili kuvya kila mundu mweavili Mwana wa Chapanga iyendelela lepi kumbudila Chapanga, ndava muni Mwana wa Chapanga akumyunga na Muhakau ihotola lepi kumkita Chindu chochoha.
Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
19 Timanyi kuvya tete ndi tavana va Chapanga, na mulima woha ulongoswa na Muhakau.
Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
20 Tete timanyili kuvya Mwana wa Chapanga amali kubwela, na mwene ndi atikitili timmanya Chapanga wa chakaka. Na tete titama mukuwungana na Chapanga wa chakaka kwa njila ya kuwungana na Mwana waki Yesu Kilisitu. Mwenuyu ndi Chapanga wa chakaka, na ndi wumi wa magono goha gangali mwishu. (aiōnios g166)
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios g166)
21 Vana vangu, mujiyangalila mkoto kugundamila chimong'omong'o.
’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.

< 1 Yohani 5 >