< Arumi 3 >

1 Hivi ni faiga gani ya bile nayo Myahudi? Na faida likokombi namani?
To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya?
2 Inogite kwa kila ndela, Awali ya goti, Ayahudi bapejilwe ufunuo buka kwa Nnongo.
Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.
3 Lakini, ibikiliwi kubina Ayahudi benge ntupu imani? Je, kotoka aminiya kwabe aminiya kwa Nnongo ba ubocho?
Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah?
4 Ntupu, badala yake, uneke Nnongo abonekane nkweli, hataitei kila mundu mmocho kati mweandikilwe, “uwese baurekana panga wa mwene haki. Mumakowe gako nawawezeshinda mewe kojingya muhukumuni”.
Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana, ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”
5 Lakini mana ibile dhambi jitu walowa bonekana haki ya Nnongo, Tubaye buli? Nnongo mdhalimu Lili papiya ukale wake, je abile nyoo? Nilongela bukana na mantiki ya kimundu.
Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.)
6 Ntupu, Ibinyoli kwa ndela gani basi Nnongo alu ukumu lunia?
Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya?
7 Namana itei kweli ya Nnongo pitya umubuchu wango piya lumbilwa kwananchima kwajili yake, mwanja namani nibii bado Kani hukumilwa kati na mwene dhambi?
Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?”
8 Mwanja namani kana tubaye, kati mwa batukopiye na kati benge mwabathibilisha panga twenda longela, “Tupange dhambi linga gananoga gaise”? Ukumilwa kwabe sawasawa.
In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.
9 Kinamani kai? Twitetee twabene? Ntupu kabisa. Kwasababu twabene tayari tutikwalaumu Ayahudi na Ayunani boti mpamo, panga babii pae ya dhambi.
To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi.
10 Haye kati mweandikilwe: “Ntupu mwene haki hata yumo.
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;
11 Ntupu mundu ywa tangite. Ntupu mundu jwa mpala Nnongo.
babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.
12 Boti bagalambwike. Bembe kwa pamope babile Ntupu maana. Ntupu ywa panga wema, kabisa, hata yumo.
Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”
13 Makolomelo gabe kati likabuli lyange kulya. Milimi yabe itikombiya. Sumu ya ng'ambo ibii pae ya maboko gabe.
“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”
14 Mikano gabe ilweli laana na uchungu.
“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”
15 Magulu Gabe gai na lubele yo pengana mwai.
“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;
16 Ubau na mateso gabi mundela gabe.
hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,
17 Bandu baa batangite lii ndela ya amani.
ba su kuma san hanyar salama ba.”
18 Ntupu kunyogopa Nnongo nnongeya minyo Gabe”.
“Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 Pano lelo tutangite kumbe chochote seliya chakilongela ilongela na balo bababile pai ya seliya. Lenga kila nkano banine, na lunga lunia yoti tuwajibike kwa Nnongo.
Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.
20 Ajii ni kwasababu ntupu mwili wawabalangilwa haki kwa kwipanga matendo ga seliya nnunge ya minyo gake. Mana pitya seliya isa kwitanga dhambi.
Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.
21 Ila bila seliya, haki ya Nnongo itanganikwa lii. Tabakijilwe kwa seliya ya manabii,
Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci.
22 iyo ni, haki ya Nnongo pitya kwa imani ya Yesu Kirisitu kwa balo boti babaaminiya. Mana ntupu tofauti.
Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci,
23 Kwasababu boti bapangite dhambi na pungukilwa na balaka ya Nnongo.
gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah,
24 Babalangilwe na haki bule kwa neema yake kwa ndila yakombolelwa na Kirisitu Yesu.
an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi.
25 Kwa mana Nnongo alikupiya Kirisitu Yesu satupatanise kwa ndela ya imani kwa myai yake. Ampiyite Kirisitu kati usaidi wa haki yake, kwasababu kutulekelea dhambi yepite
Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba
26 katika pumiliya kwake. Aga gati pitya lenga bonekana balangilwa kwa haki, mundu ywoywete kwasababu ya imani kwa Yesu.
ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.
27 kubii kwa'ko basi kwilumba? Batibagana. Kwa misingi gani? misingi ga matendo? Hata, ila kwa singi was imani.
To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya.
28 Tumbwe tuyomolwa nyanya mundu abalangilwa haki kwa imani bila makowe ga seliya.
Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba.
29 Au Nnongo ni Nnongo Ayahudi bai? je jwembe si Nnongo wabandu bange aminiya na bembe? Ngamwebile, Nabange aminiya na bembe Nnongo wabe.
Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma,
30 Mana ibi kweli Nnongo yumo, alowa kwabalangwa ya haki nababa inilwe likambi kwa imani, na bange inilwa kwa ndela ya imani.
da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin.
31 Au twenga twibadilisha seliya kwa imani? Ata! nchogo ya ago, twenga twikong'ondya seliya.
To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.

< Arumi 3 >