< Marko 1 >

1 Gono mwanzo wa Injili ya Yesu Kirisitu, mwana wa Nnongo.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 Kati mwaiandikwe ni nabii Isaya, Lola nandokubatuma asenga bango kulonge yinu, yumo apetwaa ndela yako.
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 Lukalanga wa mundu kakema mpongote, yomolyae ndela Bwana; boneyaye ndela yake”.
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Yohana ateisa, kabaatiza mpongote ni kuyegana ubatizo wa toba ku mzamaa wa sambi.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 Nnema nzima wa Sudea ni bandu bake ba Yerusalemu bayei kwake. Bai kababatizwa ni ywembe mulupondo Yordan, kabaungamana masambi gabe.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 Yohana awalage ngobo ya mayunzu ga ngamia ni nkibuno mkwisi was likengo, na alyage busi wa mwitu.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 Atelongela ni ukoya, “Abi yumo Ando isa kuoma nee, abi ni ngupu kuliko nee, nipwaa kwa ha Lita pae kuundua ilatu yake.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 Nenga niabatza kwa Mase, Ywembe abatiza mwenga kwa roho mtakatifu.
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 Yaomi lisiku eyo Yesu aisi kuoma Nazareti ya Galilaya, na atebatizwa ni roho mulupondo Yordani.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 Yesu yaagakatwike kuoma mmase abweni kunani kusalanike pala ni roho kauluka pae kunaniyake kati ngunda.
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 Ni lukalanga waomi kunani, “wenga wa manango mpendwa. Nandopulaika muno ni wenga”.
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 Mara yimo roho atikunnasimisa ayende mpongote.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 Aabii mpongote lisiku arobaini, kagiywa ni nsela. Ai pamwepe ni igongoro ya mmwitu, ni malaika kabanlola.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Tubwe kumona kuboyolwa kwa Yohana, Yesu aaisi Galilaya katangasa Injili ya Nnongo,
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 Kaakoya “muda uike, ni upwalume wa Nnongo uisi. Mubuye kwa Nnongo ni muamini mwinjili.
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 Ni kaapeta mmbwega ya mbwani ya bahari ya Galilaya, kaammona Simoni ni Andrea alongo bake Simoni kabataga mbelele yabe mmase, kwakuba baisi aubaji.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 Yesu abalogoli “muise, mungote, na niatenda aubaji ba bandu”.
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 Mara yimo baalei mbelele ni kunkota.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 Wakati Yesu ayei kutalu kasunu, ni kaammona Yakobo mwana wake Zebedayo ni YohanaNnunage, bai nngalaba kabapota mbelele.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 mara kabaakema ni bembe kabanleka tate babe nngalaba ni atenda kasi benge, kabankota.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 Apobaike Kaperaniamu lisiku ya sabato, Yesu kayingya mulisinagogi ni kuyegana.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 Batekanganya liyegano lyake kwa yelyo abi kayegana kati mundu abi ni upwalume na ayendana kwa ni aandishi menge.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 Muda gogo kwabi ni mundu mulisinagogi labe abi no nsela na ateguta.
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 Kaakoya “tubi ni selosa utenda nimwenga, Yesu wa Nazareti? uisikutuangamisa? Nandokututaga nyai wenga. Wenga wantakatifu yikayako kwa Nnongo!”
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 Yesu kaankopokya nsela ni kukoya “Nyamala ni uboke nkati yake!”
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 Ni roho njapu kantomboya pae ni kupita kalele kwa liyobe la kunani.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 Nibandu bote batekanganya eyo kabalokiyana kila yumo, “Seno kele? liyegano lyaayambe libiniupwalume? Ni nsela kunkota ago akoya!”
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 Nimayegeyo kuhusu ywembe mara yimo yalitawala kila nsengo nnema nsima wa Galilaya
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 Mara yimo baada ya kupita kunza ya Lisinagogi, Baayingi ukaya kwa Simoni ni Andrea bai ni Yakobo ni Yohana.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 Sasa akibe alwawa Simoni abiagonzike kabinya homa, mara yimo kabankokeya Yesu ubinye wake.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 Eyo kaisa, kankamwa luboko, Ni kunkagatuya, homa yaboi muyega yake ni utumbwa uudumya.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 Kitamunyo eyo lisoba liwile Abinye bote baaletikwe kwake, au babi Ni nsela kumutwe.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 Nnema nsima baikonzike pamwepe pa nlyango.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 Atealagwa Abinye banyansima mabinye mbalembale ni kupiya nsela(mahoka) banyansima, aakani mahoka kulongela maana batekuntanga.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 Aayumwike bwamba muno lubendo lukatama; aaboi ni kuyenda pandu abonekane kwa Ni mundu na kayopa oko.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 Simoni ni bote baipamwepe ni ywembe baankotike.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 Baammweni ni kunkokeya “kila yumo andokupala”.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 Atekubabakiya, “Tuboke kundukwenge, kunza ya gono nnema, ili niwese ulongela ni uko iyeya. Ndio mwalongo was kuisa pano.
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 Ayei kapeta Galilaya yote, kalongela mmasinagogi yabe Ni kukemea mahoka.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 Kaisa mundu yumo abi ni ukoma. Abi kampembela; aatengwi majua ni kunkokeya”Mana kaupala tenda nibe na nkoto”.
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 San'yingikiya, Yesu katondobeya luboko lwake ni kunkamwa kankokeya, “nipala ubebwise”.
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 Mara yimo ukoma waamboi, katenda kuba bwiso.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 Yesu atekunkopokya kwa ukale Ni kumbakiya ayende marayimo.
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 Atekumbakiya, “kanaukoye liyaulyo kwa yeyoteywa, lakini boka ukajibineye kwa kuhani, Ni upiye dhabibu kwa utakaso Musa atelagiya, katiusaidi kwabe.”
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 Ateboka Ni kutumbwa kumbakiya kila yumo nikukoya liyaulyo muno hata Yesu awesome kwa lelo kuyingya pannema kwa uhuru. Eyo atami pandu pakiiyo ni bandu baisi kuoma kila nnema.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Marko 1 >