< UZekhariya 1 >
1 Ngenyanga yesificaminwembili, ngomnyaka wesibili kaDariyusi, kwafika ilizwi leNkosi kuZekhariya, indodana kaBerekiya, indodana kaIdo umprofethi, lisithi:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 INkosi yabathukuthelela oyihlo ngentukuthelo.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Ngakho wothi kubo: Itsho njalo iNkosi yamabandla: Phendukelani kimi, itsho iNkosi yamabandla, lami ngizaphendukela kini, itsho iNkosi yamabandla.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Lingabi njengaboyihlo, abaprofethi bakuqala abamemeza kubo, besithi: Itsho njalo iNkosi yamabandla: Ake liphenduke ezindleleni zenu ezimbi lezenzweni zenu ezimbi; kodwa kabezwanga, kabangilalelanga, itsho iNkosi.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Oyihlo, bangaphi? Labaprofethi, baphila laphakade yini?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Kodwa amazwi ami lezimiso zami, engakulaya izinceku zami abaprofethi, kakubaficanga oyihlo yini? Basebephenduka bathi: Njengalokhu iNkosi yamabandla yayinakana ukukukwenza kithi, njengokwezindlela zethu lanjengokwezenzo zethu, ngokunjalo yenze kithi.
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 Ngosuku lwamatshumi amabili lane lwenyanga yetshumi lanye, okuyinyanga uShebati, ngomnyaka wesibili kaDariyusi, lafika ilizwi leNkosi kuZekhariya, indodana kaBerekiya, indodana kaIdo umprofethi, lisithi:
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 Ngabona ebusuku, khangela-ke umuntu owayegade ibhiza elibomvu, njalo wayemi phakathi kwezihlahla zamamiteli eziseliweni, lemva kwakhe kwakulamabhiza abomvu, alibhidi, lamhlophe.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 Ngasengisithi: Bayini laba, nkosi yami? Ingilosi eyayikhuluma lami yasisithi kimi: Mina ngizakutshengisa ukuthi laba bayini.
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 Umuntu owayemi phakathi kwezihlahla zamamiteli wasephendula wathi: Laba yibo iNkosi ebathumileyo ukuhamba besiya le lale emhlabeni.
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 Basebephendula ingilosi yeNkosi eyayimi phakathi kwezihlahla zamamiteli, bathi: Sihambile, saya le lale emhlabeni, khangela-ke, wonke umhlaba uhlezi uthule.
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 Ingilosi yeNkosi yasiphendula yathi: Nkosi yamabandla, koze kube nini wena ungabi lesihawu phezu kweJerusalema laphezu kwemizi yakoJuda, osuyithukuthelele okweminyaka le engamatshumi ayisikhombisa?
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 INkosi yasiphendula ingilosi eyayikhuluma lami ngamazwi amahle, amazwi aduduzayo.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 Ngakho ingilosi eyayikhuluma lami yathi kimi: Memeza, usithi: Itsho njalo iNkosi yamabandla: Ngilobukhwele ngeJerusalema langeZiyoni ngobukhwele obukhulu.
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 Njalo ngiyathukuthela ngentukuthelo enkulu ngezizwe ezonwabileyo; ngoba mina ngizondile kancinyane, kodwa zona zancedisa ngasebubini.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Ngalokho, itsho njalo iNkosi: Ngibuyele eJerusalema ngilezihawu; indlu yami izakwakhiwa kuyo, itsho iNkosi yamabandla, lentambo yokulinganisa izakwelulwa phezu kweJerusalema.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Phinda umemeze, usithi: Itsho njalo iNkosi yamabandla: Imizi yami isezasatshalaliswa ngokuhle; njalo iNkosi isezaduduza iZiyoni, isezayikhetha iJerusalema.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Ngasengiphakamisa amehlo ami, ngabona, khangela-ke, impondo ezine.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 Ngasengisithi kuyo ingilosi eyayikhuluma lami: Kuyini lokhu? Yasisithi kimi: Lezi zimpondo ezihlakaze uJuda, uIsrayeli, leJerusalema.
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 INkosi yasingitshengisa ingcitshi ezine.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 Ngasengisithi: Lezi zizekwenzani? Yasikhuluma isithi: Lezi zimpondo ezihlakaze uJuda, kwaze kwangabi lomuntu ophakamisa ikhanda lakhe; kodwa lezi zize ukuzethusa, ukulahla izimpondo zabezizwe, ezaphakamisa uphondo lumelene lelizwe lakoJuda ukulihlakaza.
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”