< UZekhariya 10 >
1 Celani eNkosini izulu ngesikhathi sezulu langemuva; iNkosi yenza imibane, ibanike izihlambo zezulu, kulolo lalolo uhlaza egangeni.
Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
2 Ngoba izithombe zikhulume ize, labavumisi babone amanga, balandisa amaphupho ayinkohliso, baduduza ngokuyize. Ngakho-ke bazihambela njengezimvu, badubeka, ngoba kwakungelamelusi.
Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
3 Intukuthelo yami yavutha imelene labelusi, ngajezisa izimpongo; ngoba iNkosi yamabandla izawuhambela umhlambi wayo, indlu kaJuda; ibenze babe njengebhiza layo elihlekazi empini.
“Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
4 Kwaphuma kuye igumbi, kuye isikhonkwane, kuye idandili lempi, kuye wonke umcindezeli ndawonye.
Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
5 Futhi bazakuba njengamaqhawe anyathela odakeni lwezitalada empini; njalo bazakulwa, ngoba iNkosi ilabo, bayangise abagadi bamabhiza.
Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
6 Njalo ngizaqinisa indlu kaJuda, ngisindise indlu kaJosefa, ngibabuyise, ngoba ngilesihawu kubo. Njalo bazakuba njengokungathi kangizanga ngibalahle; ngoba ngiyiNkosi uNkulunkulu wabo, ngibezwe.
“Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
7 Njalo amaEfrayimi azakuba njengeqhawe, lenhliziyo yawo ithokoze njengangewayini. Yebo abantwana bawo bazakubona, bathokoze; inhliziyo yawo izathokoza eNkosini.
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
8 Ngizabatshayela ukhwelo, ngibabuthe; ngoba ngibahlengile; njalo bazakwanda njengoba sebandile.
Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
9 Njalo ngizabahlanyela phakathi kwezizwe, bangikhumbule endaweni ezikhatshana; baphile labantwana babo, baphenduke.
Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
10 Ngibabuyise bevela elizweni leGibhithe, ngibaqoqe baphume eAsiriya; ngibalethe elizweni leGileyadi leLebhanoni, kodwa kabayikutholelwa ndawo.
Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
11 Njalo uzadabula olwandle lenhlupheko, atshaye amagagasi olwandle, lazo zonke izinziki zomfula zizakoma; lokuzigqaja kweAsiriya kwehliswe, lentonga yobukhosi yeGibhithe isuke.
Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
12 Njalo ngizabaqinisa eNkosini; bahambe besiya le lale ebizweni layo, itsho iNkosi.
Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.