< Isambulo 13 >

1 Ngasengisima etshebetshebeni lolwandle; ngasengibona isilo sikhuphuka olwandle, silamakhanda ayisikhombisa lempondo ezilitshumi, laphezu kwempondo zaso imiqhele elitshumi, laphezu kwamakhanda aso kulebizo lenhlamba.
Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
2 Lesilo engasibonayo sasinjengengwe, lenyawo zaso zazinjengezebhere, lomlomo waso unjengomlomo wesilwane. Njalo umgobho wasinika amandla awo, lesihlalo sawo sobukhosi, legunya elikhulu.
Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
3 Ngasengibona elinye lamakhanda aso kungathi lilimele okokufa; lenxeba laso lokufa selapholiswa; umhlaba wonke wasumangala ngemva kwesilo;
Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
4 basebewukhonza umgobho owasinika isilo amandla, basebesikhonza isilo, besithi: Ngubani ofanana lesilo? Ngubani ongalwa laso?
Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
5 Kwasekunikelwa kuso umlomo wokukhuluma izinto ezinkulu lezinhlamba, kwasekunikelwa kuso amandla okusebenza inyanga ezingamatshumi amane lambili.
Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
6 Sasesivula umlomo waso ukuhlambaza okumelane loNkulunkulu, lokuhlambaza ibizo lakhe, lethabhanekele lakhe, lalabo abahlezi ezulwini.
Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
7 Kwasekunikelwa kuso ukuthi silawule impi labangcwele, lokubanqoba; kwasekunikelwa kuso amandla phezu kwawo wonke umhlobo lolimi lesizwe.
Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
8 Labo bonke abakhileyo emhlabeni bazasikhonza, labo amabizo abo angabhalwanga egwalweni lwempilo lweWundlu elahlatshwayo selokhu kwasekelwa umhlaba.
Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
9 Uba umuntu elendlebe, kezwe.
Duk mai kunne ji, bari yă ji.
10 Uba umuntu ethumba, uya ekuthunjweni; uba umuntu ebulala ngenkemba, yena kumele abulawe ngenkemba. Lapha kulokubekezela lokholo lwabangcwele.
Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
11 Ngasengibona esinye isilo sisenyuka emhlabeni, sasilempondo ezimbili njengewundlu, sasesikhuluma njengomgobho.
Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
12 Njalo sasebenzisa wonke amandla esilo sokuqala phambi kwaso, futhi senza ukuthi umhlaba labakhileyo kuwo bakhonze isilo sokuqala, esinxeba laso lokufa lapholiswa.
Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
13 Sasesisenza izibonakaliso ezinkulu, saze senza ukuthi lomlilo wehle uvela ezulwini uze emhlabeni, phambi kwabantu.
Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
14 Sasesiduhisa abakhileyo emhlabeni ngalezozibonakaliso ezanikelwa kuso ukuzenza phambi kwesilo, sisithi kwabakhileyo emhlabeni, kabasenzele umfanekiso isilo ebesilenxeba lenkemba, sasesiphila.
Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
15 Sanikwa futhi ukupha umfanekiso wesilo umoya, ukuze umfanekiso wesilo lawo ukhulume, besesisenza ukuthi bonke abangakhonziyo umfanekiso wesilo babulawe.
Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
16 Sasesisenza bonke, abancinyane labakhulu, labanothileyo labayanga, labakhululekileyo lezigqili, ukuthi baphiwe uphawu esandleni sabo sokunene, loba emabunzini abo,
Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
17 ukuze kungabi khona olakho ukuthenga loba ukuthengisa, ngaphandle kwalowo olophawu, loba ibizo lesilo loba inombolo yebizo laso.
don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
18 Nansi inhlakanipho. Olokuqedisisa kabale inombolo yesilo; ngoba iyinombolo yomuntu, lenombolo yaso ingamakhulu ayisithupha lamatshumi ayisithupha lesithupha.
Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.

< Isambulo 13 >