< Amahubo 97 >
1 INkosi iyabusa; kawuthokoze umhlaba, kazijabule izihlenge ezinengi.
Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
2 Amayezi lomnyama kuyiphahlile; ukulunga lesahlulelo kuyisisekelo sesihlalo sayo sobukhosi.
Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
3 Umlilo uhamba phambi kwayo, utshisa izitha zayo inhlangothi zonke.
Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
4 Imibane yayo ikhanyisa umhlaba; umhlaba wabona, wathuthumela.
Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
5 Izintaba zancibilika njengengcino phambi kweNkosi, phambi kweNkosi yomhlaba wonke.
Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
6 Amazulu atshumayela ukulunga kwayo, labantu bonke babona inkazimulo yayo.
Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
7 Bayayangeka bonke abakhonza izithombe, abazikhukhumeza ngezithixo; ikhonzeni, lonke bonkulunkulu.
Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
8 IZiyoni yezwa, yathokoza, lamadodakazi akoJuda athaba ngenxa yezahlulelo zakho, Nkosi.
Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
9 Ngoba wena, Nkosi, uphakeme phezu komhlaba wonke, uphakanyiswe kakhulu phezu kwabonkulunkulu bonke.
Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
10 Lina elithanda iNkosi, zondani okubi; iyagcina imiphefumulo yabangcwele bayo, ibakhulule esandleni sababi.
Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
11 Ukukhanya kuhlanyelelwe olungileyo, lentokozo abaqotho ngenhliziyo.
An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
12 Thokozani eNkosini, lina balungileyo, libonge ekukhumbuleni ubungcwele bayo.
Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.