< Amahubo 81 >

1 Hlabelani kakhulu kuNkulunkulu amandla ethu, lihlokome ngentokozo kuNkulunkulu kaJakobe.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Thathani ingoma, lilethe isigujana, ichacho elimnandi kanye logubhu lwezintambo.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Vuthelani uphondo ekuthwaseni kwenyanga, esikhathini esimisiweyo, ngosuku lomkhosi wethu.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Ngoba lokho kuyisimiso kuIsrayeli, umthetho kaNkulunkulu kaJakobe.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Wakumisa kwaba yibufakazi kuJosefa, ekuphumeni kwakhe emelene lelizwe leGibhithe; ngezwa ulimi engingalwaziyo.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Ngasusa ihlombe lakhe emthwalweni; izandla zakhe zakhululwa ezimbizeni.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Wakhala usenhluphekweni, ngakukhulula; ngakuphendula ekusithekeni komdumo; ngakuhlola emanzini eMeriba. (Sela)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Zwana, sizwe sami, ngizafakaza kuwe, Israyeli, aluba ungangilalela.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Kakungabi khona phakathi kwakho unkulunkulu wezizweni, njalo ungakhonzi unkulunkulu wezizweni.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Mina ngiyiNkosi, uNkulunkulu wakho, owakwenyusa usuka elizweni leGibhithe. Khamisa umlomo wakho ube banzi, njalo ngizawugcwalisa.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Kodwa abantu bami kabalilalelanga ilizwi lami; loIsrayeli kavumelananga lami.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Ngakho ngabanikela enkanini yenhliziyo yabo, ukuze bahambe kumacebo abo.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Kungathi abantu bami bebengangilalela, uIsrayeli ahambe endleleni zami!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Masinyane bengingazehlisela phansi izitha zabo, ngiphendulele isandla sami kwabamelene labo.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Abayizondayo iNkosi bangatshotshobala phambi kwayo ngokuzenzisa, kodwa isikhathi sabo besizakuba phakade.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Wayezabondla ngamanono engqoloyi; njalo bengizakusuthisa ngoluju oluvela edwaleni.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Amahubo 81 >