< Amahubo 78 >

1 Lalelani, bantu bami, umthetho wami, libeke indlebe yenu emazwini omlomo wami.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Ngizavula umlomo wami ngomfanekiso, ngikhuphe izimfihlakalo zendulo,
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 esizizwileyo lesizaziyo, obaba abasitshela zona.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Kasiyikuzifihlela abantwana babo, kusizukulwana esilandelayo, silandisa izindumiso zeNkosi, lamandla ayo, lezimangaliso ezenzileyo.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Ngoba wamisa ubufakazi koJakobe, wabeka umlayo koIsrayeli, awulaya obaba, ukuze bawazise abantwana babo,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 ukuze isizukulwana esilandelayo sazi, abantwana abazazalwa, basukume batshele abantwana babo,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 ukuze babeke ithemba labo kuNkulunkulu, bangayikhohlwa imisebenzi kaNkulunkulu, kodwa bagcine imithetho yakhe;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 njalo bangabi njengaboyise, isizukulwana esilenkani lesivukelayo, isizukulwana esingaqondisanga inhliziyo yaso, lesimoya waso ungathembekanga kuNkulunkulu.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Abantwana bakoEfrayimi, behlomile betshoka ngamadandili, babuyela emuva mhla wempi.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Kabasilondolozanga isivumelwano sikaNkulunkulu, bala ukuhamba emlayweni wakhe.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Bakhohlwa izenzo zakhe lezimangaliso zakhe ayebatshengisa zona.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Phambi kwaboyise wenza isimangaliso elizweni leGibhithe, egangeni leZowani.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Waqhekeza ulwandle, wabachaphisa, wenza amanzi ema njengenqumbi.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Wabakhokhela ngeyezi emini, lebusuku bonke ngokukhanya komlilo.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Waqhekeza amadwala enkangala, wabanathisa kungathi kuvela ezinzikini ezinkulu.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Waseveza izifula edwaleni, wenza amanzi ehla njengemifula.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Kodwa baphinda futhi ukona kuye, ngokumvukela oPhezukonke enkangala.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Bamlinga uNkulunkulu enhliziyweni yabo ngokucela ukudla kwenkanuko yabo.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Basebekhuluma bemelene loNkulunkulu bathi: UNkulunkulu angalungisa itafula enkangala yini?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Khangela, watshaya idwala, kwampompoza amanzi, lezifula zagabha; anganika lesinkwa yini? angalungisela abantu bakhe inyama na?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Ngakho iNkosi yezwa yathukuthela; umlilo wasubaselwa uJakobe, njalo lolaka lwavukela uIsrayeli,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 ngoba kabakholwanga kuNkulunkulu, kabathembanga esindisweni lwakhe.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Lanxa walaya amayezi ngaphezulu, wavula iminyango yamazulu,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 wabanisela imana ukuthi badle, wabapha amabele amazulu.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Umuntu wadla isinkwa sabalamandla; wabathumela ukudla ukuze basuthe.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Wenza umoya wempumalanga wavunguza emazulwini; langamandla akhe waqhuba umoya weningizimu.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Wasenisela phezu kwabo inyama njengothuli, lenyoni ezilempiko njengetshebetshebe lolwandle;
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 wazenza zawela phakathi kwenkamba yabo, zagombolozela indawo zabo zokuhlala.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Ngakho badla basutha kakhulu, ngoba wabalethela isiloyiso sabo.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Kabehlukananga lenkanuko yabo; ukudla kusesemlonyeni wabo,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 ulaka lukaNkulunkulu lwaselubavukela, wabulala kwabakhulupheleyo babo, watshaya abakhethiweyo bakoIsrayeli.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Kulokhu konke bajinga besona, njalo kabakholwanga ngenxa yezimangaliso zakhe.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Ngakho waziqeda izinsuku zabo ngeze, leminyaka yabo ovalweni.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Lapho ebabulala, bamdinga, baphenduka, bamdingisisa uNkulunkulu.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Bakhumbula ukuthi uNkulunkulu ulidwala labo, loNkulunkulu oPhezukonke ungumhlengi wabo.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Kodwa bamyenga ngomlomo wabo, baqamba amanga kuye ngolimi lwabo.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Ngoba inhliziyo yabo yayingaqondanga kuye, njalo bengathembekanga esivumelwaneni sakhe.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Kodwa yena elesihawu wathethelela ububi babo, kababhubhisanga; yebo, kanengi walunqanda ulaka lwakhe, kakuvusanga konke ukuthukuthela kwakhe.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Ngoba wakhumbula ukuthi bayinyama, umoya odlulayo, ongabuyiyo.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Kanengi kangakanani bemvukela ehlane, bemdabukisa enkangala.
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Yebo baphenduka bamlinga uNkulunkulu, bamdabukisa oNgcwele kaIsrayeli.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Kabasikhumbulanga isandla sakhe, usuku abahlenga ngalo esitheni.
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Ukuthi wamisa njani izibonakaliso zakhe eGibhithe, lezimangaliso zakhe emmangweni weZowani,
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 lokuthi waphendula imifula yabo yaba ligazi, lezifula zabo, ukuze banganathi.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Wathumela phakathi kwabo umtshitshi wezibawu, ezabadlayo, lamaxoxo ababhubhisayo.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Wasenika imihogoyi isivuno sabo, lomsebenzi wabo isikhonyane.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Wabulala ivini labo ngesiqhotho, lemikhiwa yabo yesikhamore ngongqwaqwane.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Wasenikela izifuyo zabo esiqhothweni, lemihlambi yabo kuyo imibane.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Waphosela phezu kwabo ukuvutha kolaka lwakhe, ukuthukuthela, lokucunuka, lokuhlupheka, ngokuthuma izithunywa zobubi.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Walungisela ulaka lwakhe indlela, kanqandanga umphefumulo wabo ekufeni, kodwa wanikela impilo yabo kumatshayabhuqe wesifo.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Wasetshaya wonke amazibulo eGibhithe, okokuqala kwamandla emathenteni kaHamu.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Wasebakhupha abantu bakhe njengezimvu, wabakhokhela enkangala njengomhlambi.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Wasebakhokhela bephephile ukuze bangesabi; kodwa ulwandle lwasibekela izitha zabo.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Wasebafikisa emkhawulweni wendawo yakhe engcwele, le intaba, isandla sakhe sokunene esayizuzayo.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Wasebaxotsha abezizwe phambi kwabo; wababela ilifa ngomzila, wahlalisa izizwe zakoIsrayeli emathenteni azo.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Kanti bamlinga, bamvukela uNkulunkulu oPhezukonke, kabazigcinanga izifakazelo zakhe.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Kodwa babuyela emuva, benza ngokungathembeki njengaboyise, baphanjulwa njengedandili elikhohlisayo.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Ngoba bamthukuthelisa ngezindawo zabo eziphakemeyo, bavusa umona wakhe ngezithombe zabo ezibaziweyo.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 UNkulunkulu esizwa wathukuthela, wamenyanya kakhulu uIsrayeli.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Ngakho walitshiya ithabhanekele leShilo, ithente alimisa phakathi kwabantu.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Wasenikela amandla akhe ekuthunjweni, lenkazimulo yakhe esandleni sesitha.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Wasenikela abantu bakhe enkembeni, waselithukuthelela ilifa lakhe.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Umlilo waqeda amajaha abo, lezintombi zabo kazihlatshelelwanga.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Abapristi babo bawa ngenkemba, labafelokazi babo kabalilanga.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Khona iNkosi yavuka njengobelele, njengeqhawe eliklabalala ngenxa yewayini.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Yazitshaya izitha zayo emuva, yazithela ihlazo phakade.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Yasilahla ithente likaJosefa, kayikhethanga isizwe sakoEfrayimi.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Kodwa yakhetha isizwe sakoJuda, intaba yeZiyoni eyithandayo.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Yayakha indlu yayo engcwele njengezingqonga, njengomhlaba ewusekeleyo kuze kube nininini.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Yasikhetha uDavida inceku yayo, yamthatha ezibayeni zezimvu;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 ekulandeleni izimvukazi ezenyisayo, yamletha ukwelusa uJakobe abantu bayo, loIsrayeli ilifa layo.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Njalo wabelusa njengobuqotho benhliziyo yakhe, wabakhokhela ngobugabazi bezandla zakhe.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Amahubo 78 >