< Amahubo 50 >
1 USomandla, uNkulunkulu, iNkosi, ukhulumile, ubiza umhlaba kusukela ekuphumeni kwelanga kuze kube sekutshoneni kwalo.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 EseZiyoni, ukuphelela kobuhle, uNkulunkulu ukhanyile.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 UNkulunkulu wethu uzakuza, kayikuthula; umlilo phambi kwakhe uzaqothula, enhlangothini zonke zakhe kuzakuba lesiphepho esikhulu.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Uzabiza amazulu ephezulu, lomhlaba, ukwahlulela abantu bakhe.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Buthelani kimi abangcwele bami, abenza isivumelwano lami ngomhlatshelo.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Lamazulu azatshumayela ukulunga kwakhe, ngoba uNkulunkulu ngokwakhe ungumahluleli. (Sela)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Zwanini bantu bami, ngizakhuluma; Israyeli, ngizafakaza ngimelene lawe. NginguNkulunkulu, uNkulunkulu wakho.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Kangikusoli ngenxa yemihlatshelo yakho; leminikelo yakho yokutshiswa ihlala iphambi kwami.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Kangiyikuthatha ijongosi elivela emzini wakho, lezimpongo ezivela ezibayeni zakho.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Ngoba ngeyami yonke inyamazana yehlathi, izinkomo ezisentabeni eziyizinkulungwane.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Ngiyazazi izinyoni zonke zezintaba, lezilo zommango zikimi.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Uba bengilambile, bengingayikukutshela, ngoba umhlaba ngowami lokugcwala kwawo.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Ngizayidla yini inyama yezinkunzi, kumbe nginathe igazi lezimpongo?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Nikela kuNkulunkulu umhlatshelo wokubonga, ukhokhe izithembiso zakho koPhezukonke.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Ungibize osukwini lokuhlupheka, ngizakukhulula, ubusungidumisa.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Kodwa komubi uNkulunkulu uthi: Ulani lokuthi utshumayele izimiso zami, kumbe uthathe isivumelwano sami emlonyeni wakho?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Ngoba wena uzonda ukuqondiswa, ulahla amazwi ami emva kwakho.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Uba ubona isela, uthokozelana lalo, lesabelo sakho sisezifebeni.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Umlomo wakho uyawunikela ebubini, lolimi lwakho luqambe inkohliso.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Uhlala ukhulume umelene lomfowenu, uhlebe indodana kanyoko.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Lezizinto uzenzile, ngathula; wacabanga ukuthi nginjengawe kanye. Ngizakukhuza, ngikuhlele phambi kwamehlo akho.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Kuqapheleni-ke lokhu, lina elikhohlwa uNkulunkulu, hlezi ngilidabule, kungabi khona okukhululayo.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Onikela umnikelo wokubonga uyangidumisa; lolungisa indlela yakhe ngizambonisa usindiso lukaNkulunkulu.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”