< Amahubo 44 >

1 Nkulunkulu, sizwile ngendlebe zethu, obaba basitshelile, umsebenzi owawenza ensukwini zabo, ensukwini zendulo.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Wena ngesandla sakho wazixotsha izizwe elifeni, wabahlanyela bona; wazihlupha izizwe, kodwa wabasabalalisa bona.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Ngoba kabadlanga ilifa lelizwe ngenkemba yabo, lengalo yabo kayibasindisanga, kodwa isandla sakho sokunene, lengalo yakho, lokukhanya kobuso bakho, ngoba wawubathanda.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Wena uyiNkosi yami, Nkulunkulu; laya ukukhululwa kukaJakobe.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Ngawe sizadudula izitha zethu; ngebizo lakho sizabanyathelela phansi abasivukelayo.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Ngoba kangithembeli kulo idandili lami, lenkemba yami kayiyikungisindisa.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Kodwa usisindisile ezitheni zethu, wayangisa abasizondayo.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 KuNkulunkulu siyazincoma usuku lonke; lebizo lakho sizalidumisa kuze kube nininini. (Sela)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Kodwa ulahlile wasiyangisa, njalo kawuphumi lamabutho ethu.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Usenze ukuthi sibuyele emuva sisuka esitheni; labasizondayo baziphangela.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Usinikele njengezimvu zokudliwa, wasichithachitha phakathi kwezizwe.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Uthengisile abantu bakho ngokungelanotho, awuzuzanga lutho ngentengo yabo.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Usenze saba lihlazo kwabakhelene lathi, inhlekisa lendumazo kwabasiphahlileyo.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Usenze saba yisiga phakathi kwezizwe, ukunikinwa kwekhanda phakathi kwabantu.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Usuku lonke ukudunyazwa kwami kuphambi kwami, lehlazo lobuso bami lingigubuzele,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 ngenxa yelizwi lomgconi lomhlambazi, ngenxa yesitha lomphindiseli.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Konke lokhu kusehlele, kube kanti kasikukhohlwanga, kasenzanga ngenkohliso esivumelwaneni sakho.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Inhliziyo yethu kayibuyelanga emuva, lezinyathelo zethu kaziphambukanga emkhondweni wakho,
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 lanxa usichobozile endaweni yamaganyana, usembese ngethunzi lokufa.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Uba besilikhohliwe ibizo likaNkulunkulu wethu, loba selulela izandla zethu kunkulunkulu wezizweni,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 uNkulunkulu ubengayikukuhlola lokhu yini? Ngoba uyayazi imfihlo yenhliziyo.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Yebo, ngenxa yakho siyabulawa usuku lonke, kuthiwa sinjengezimvu zokuhlatshwa.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Phaphama, ulaleleni, Nkosi? Vuka, ungalahli kokuphela.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Ufihlelani ubuso bakho, ukhohlwe ukuhlupheka kwethu locindezelo lwethu?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Ngoba umphefumulo wethu ukhothamele othulini, isisu sethu sinamathela emhlabathini.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Sukumela usizo lwethu, usihlenge ngenxa yomusa wakho.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Amahubo 44 >