< Amahubo 33 >
1 Thokozani eNkosini, balungileyo. Ukudumisa kubafanele abaqotho.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Dumisani iNkosi ngechacho, lihlabelele kuyo ngogubhu olulentambo ezilitshumi.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Ihlabeleleni ingoma entsha, litshaye kuhle ngenhlokomo.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 Ngoba ilizwi leNkosi liqotho, lomsebenzi wayo wonke ngowobuqotho.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Ithanda ukulunga lesahlulelo; umhlaba ugcwele umusa weNkosi.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Ngelizwi leNkosi amazulu enziwa, lalo lonke ibutho lawo ngomoya womlomo wayo.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Ibuthelela amanzi olwandle njengenqumbi, ifake inziki eziphaleni.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Umhlaba wonke kawuyesabe iNkosi, bonke abakhileyo bomhlaba kabathuthumele ngayo.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 Ngoba yona yakhuluma, kwaba khona; yona yalaya, kwema.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 INkosi ichitha icebo lezizwe, iphuthisa imicabango yabantu.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 Icebo leNkosi limi kuze kube nininini, imicabango yenhliziyo yayo ezizukulwaneni ngezizukulwana.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Sibusisiwe isizwe esiNkulunkulu waso yiNkosi, abantu ebakhethileyo baba yilifa layo.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 INkosi iyakhangela phansi isemazulwini, ibone bonke abantwana babantu.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Isendaweni emisiweyo yokuhlala kwayo ikhangela bonke abakhileyo bomhlaba.
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 Ibumba inhliziyo yabo bonke, inanzelele zonke izenzo zabo.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 Kayikho inkosi esindiswa yibunengi bebutho, iqhawe kalikhululwa ngamandla amakhulu.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Ibhiza liyize ekunqobeni, njalo kalikhululi ngobukhulu bamandla alo.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Khangela, ilihlo leNkosi liphezu kwabayesabayo, kwalabo abathembela emuseni wayo,
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 ukukhulula umphefumulo wabo ekufeni, lokubaphilisa endlaleni.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Umphefumulo wethu ulindela iNkosi; ilusizo lwethu lesihlangu sethu.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 Ngoba inhliziyo yethu izathokoza kuyo, ngoba sithembele ebizweni layo elingcwele.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Umusa wakho, Nkosi, kawube phezu kwethu, njengokulindela kwethu kuwe.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.