< Amahubo 29 >

1 Inikeni iNkosi, lina madodana abalamandla, inikeni iNkosi udumo lamandla.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Inikeni iNkosi udumo lwebizo layo, likhothame eNkosini ebuhleni bobungcwele.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Ilizwi leNkosi liphezu kwamanzi; uNkulunkulu wenkazimulo uyaduma; iNkosi iphezu kwamanzi amanengi.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 Ilizwi leNkosi lilamandla, ilizwi leNkosi lilobukhosi.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 Ilizwi leNkosi lephula imisedari, yebo, iNkosi yephula imisedari yeLebhanoni.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Yenza yona-ke iqolotshe njengethole, iLebhanoni leSiriyoni njengethole lenyathi.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Ilizwi leNkosi lidabula amalangabi omlilo.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 Ilizwi leNkosi lizamazamisa inkangala, iNkosi izamazamisa inkangala yeKadeshi.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Ilizwi leNkosi lizalisa izimpala, lihlubule amahlathi; lethempelini layo konke kuthi: Udumo.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 UJehova uhlezi phezu kukazamcolo, yebo, uJehova uhlezi eyiNkosi kuze kube nininini.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 INkosi izanika abantu bayo amandla; iNkosi ibusise abantu bayo ngokuthula.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Amahubo 29 >