< Amahubo 22 >

1 Nkulunkulu wami, Nkulunkulu wami, ungitshiyeleni na? Ukhatshana lokungisiza, lamazwi okubhonga kwami?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Nkulunkulu wami, ngiyakhala emini, kodwa kawungiphenduli, lebusuku, kodwa kangilakho ukuthula.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Kodwa wena ungcwele, ohlezi ezibongweni zikaIsrayeli.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Obaba bethu bathemba kuwe, bathemba, wasubakhulula.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Bakhala kuwe, bakhululwa; bathembela kuwe, kabayangekanga.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Kodwa ngingumswenya, kangisuye muntu, ihlazo labantu, ngeyiswa ngabantu.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Bonke abangibonayo bayangihleka usulu, bakhamisa indebe, banikine ikhanda,
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 besithi: Wathembela eNkosini; kayimkhulule, imophule, ngoba yathokoza kuye.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Kodwa nguwe owangikhupha esiswini, wangenza ngathemba ngisemabeleni kamama.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Ngalahlelwa phezu kwakho kusukela esizalweni; kusukela esiswini sikamama unguNkulunkulu wami.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Ungabi khatshana lami, ngoba uhlupho luseduze, ngoba kakho osizayo.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Izinkunzi ezinengi zingihanqile, ezilamandla zeBashani zingizingelezele.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Zangikhamisela umlomo wazo, isilwane esiphangayo lesibhongayo.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Ngithululiwe njengamanzi, lamathambo ami wonke ehlukene; inhliziyo yami injengengcino, incibilikile phakathi kwemibilini yami.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Amandla ami omile njengodengezi, lolimi lwami lunamathele emihlathini yami; ungibeke ethulini lokufa.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Ngoba izinja zingigombolozele; inhlangano yababi ingihanqile; izandla zami lenyawo zami bazibhobozile.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Ngingabala wonke amathambo ami; bona bayakhangela bayangijolozela.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Babelana izigqoko zami, benza inkatho yokuphosa ngezembatho zami.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Kodwa, wena Nkosi, ungabi khatshana; mandla ami, phangisa ukungisiza.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Khulula umphefumulo wami kuyo inkemba, wona wodwa owami emandleni enja.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Ngisindisa emlonyeni wesilwane; ngoba empondweni zezinyathi ungiphendule.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Ngizalandisa ibizo lakho kubafowethu, phakathi kwebandla ngizakudumisa.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Lina elesaba iNkosi, idumiseni; lonke nzalo kaJakobe, ihlonipheni; liyesabe, lonke nzalo kaIsrayeli.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Ngoba kayidelelanga kayinengwanga yinhlupheko yohluphekayo; njalo kayimfihlelanga ubuso bayo; kodwa lapho ekhala kuyo, yezwa.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Indumiso yami izakuba ngawe ebandleni elikhulu; ngizakhokha izifungo zami phambi kwabayesabayo.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Abamnene bazakudla basuthe; bazayidumisa iNkosi labo abayidingayo. Inhliziyo yenu izaphila kuze kube phakade.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Imikhawulo yonke yomhlaba izakhumbula, iphendukele eNkosini; lezizukulwana zonke zezizwe zizakhonza phambi kwakho.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Ngoba umbuso ungoweNkosi, njalo iyabusa phakathi kwezizwe.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Bonke abakhulupheleyo bomhlaba bazakudla bakhonze; bonke abehlela othulini bazakhothama phambi kwayo, longagcini umphefumulo wakhe uphila.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Inzalo izayikhonza; izabalelwa eNkosini kuso isizukulwana.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Bazakuza bamemezele ukulunga kwayo ebantwini abazazalwa, ukuthi ikwenzile.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Amahubo 22 >