< Amahubo 120 >
1 Ekuhluphekeni kwami ngakhala eNkosini, yangiphendula.
Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
2 Nkosi, khulula umphefumulo wami kundebe zamanga, kulimi lwenkohliso.
Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
3 Uzanikwani, njalo kuzakwengezelelwani kuwe, limi lwenkohliso?
Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
4 Imitshoko ebukhali yeqhawe, lamalahle avuthayo esihlahla serotemu!
Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
5 Maye kimi, ngoba ngihlala njengowezizwe koMesheki, ngihlala emathenteni eKedari!
Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
6 Umphefumulo wami sekukade wahlala laye ozonda ukuthula.
Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
7 Ngingowokuthula, kodwa lapho ngikhuluma, bangabempi.
Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.