< Amahubo 106 >

1 Dumisani iNkosi! Ibongeni iNkosi ngoba ilungile, ngoba umusa wayo umi kuze kube nininini.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Ngubani ongalandisa izenzo ezilamandla zeNkosi, azwakalise yonke indumiso yayo?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Babusisiwe abagcina izahlulelo, owenza ukulunga ngaso sonke isikhathi.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Ngikhumbule, Nkosi, ngothando olalo kubantu bakho; ngethekelele ngosindiso lwakho;
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 ukuze ngibone okuhle kwabakhethiweyo bakho, ukuze ngithokoze entokozweni yesizwe sakho, ukuze ngizincome kanye lelifa lakho.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Sonile kanye labobaba, senze okubi, senza ngenkohlakalo.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Obaba eGibhithe kabaqedisisanga izimangaliso zakho; kabakhumbulanga ubunengi bezisa zakho; kodwa benza umvukela elwandle, eLwandle oluBomvu.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Loba kunjalo wabakhulula ngenxa yebizo lakhe, ukuze azise amandla akhe.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Wasekhuza uLwandle oluBomvu, lwatsha; wasebahambisa phakathi kwezinziki njengenkangala.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Wasebasindisa esandleni somzondi, wabahlenga esandleni sesitha.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Amanzi asibekela izitha zabo; kakusalanga loyedwa kuzo.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Basebekholwa amazwi akhe, bahlabelela indumiso yakhe.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Baphanga bakhohlwa imisebenzi yakhe, kabalindelanga iseluleko sakhe.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Kodwa bakhanuka lokukhanuka ehlane, bamlinga uNkulunkulu enkangala.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Wasebanika isicelo sabo, kodwa wathumela ukucaka emphefumulweni wabo.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Basebesiba lomhawu ngoMozisi enkambeni, ngoAroni ongcwele weNkosi.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Umhlaba wavuleka waginya uDathani, wasibekela iqembu likaAbiramu.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Lomlilo wavutha eqenjini labo, ilangabi latshisa abakhohlakeleyo.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Benza ithole eHorebe, bakhonza isithombe esibunjwe ngokuncibilikisa.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Basebeguqula inkazimulo yabo yaba yisifaniso senkabi edla utshani.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Bamkhohlwa uNkulunkulu umsindisi wabo, owayenze izinto ezinkulu eGibhithe,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 izimangaliso elizweni likaHamu; izinto ezesabekayo eLwandle oluBomvu.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Ngakho wathi uzababhubhisa, ngaphandle kokuthi uMozisi okhethiweyo wakhe wayemile ekufohleni phambi kwakhe ukuphendula ulaka lwakhe ukuze angababhubhisi.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Yebo, baleyisa ilizwe elihle, kabalikholwanga ilizwi lakhe.
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 Kodwa bakhonona emathenteni abo, kabalilalelanga ilizwi leNkosi.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Ngakho waphakamisa isandla sakhe emelene labo, ukubawisa enkangala,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 lokuwisa inzalo yabo phakathi kwezizwe, lokubahlakaza emazweni.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Basebezihlanganisa loBhali-Peyori, badla imihlatshelo yabafileyo.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Basebemthukuthelisa ngezenzo zabo, lenhlupheko yafohlela kibo.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Kwasekusukuma uPhinehasi, wenza isigwebo, inhlupheko yasimiswa.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Lokhu kwasekubalelwa kuye kube yikulunga, esizukulwaneni ngesizukulwana kuze kube nininini.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Basebemthukuthelisa emanzini empikisano, kwaze kwaba kubi kuMozisi ngenxa yabo.
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Ngoba bacunula umoya wakhe, waze wakhuluma ngamawala ngendebe zakhe.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Kabazibhubhisanga izizwe, iNkosi eyayibatshele ngazo.
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 Kodwa bazihlanganisa lezizwe, bafunda imisebenzi yazo.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Basebekhonza izithombe zazo ezaba ngumjibila kubo.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Lamadodana abo lamadodakazi abo bawahlabela amadimoni.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Bachitha igazi elingelacala, igazi lamadodana abo lamadodakazi abo, abawahlabela izithombe zeKhanani; lelizwe langcoliswa ngegazi elinengi.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Basebengcola ngemisebenzi yabo, baphinga ngezenzo zabo.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Ngakho ulaka lweNkosi lwabavuthela abantu bayo, yanengwa yilifa layo.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Yabanikela esandleni sezizwe, lababazondayo bababusa.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Lezitha zabo zabacindezela, basebethotshiswa ngaphansi kwesandla sazo.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Yabakhulula kanengi; kodwa bona bayivukela ngecebo labo, behliswa ngobubi babo.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Loba kunjalo yabona ukuhlupheka kwabo, lapho isizwa ukukhala kwabo.
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Yabakhumbulela isivumelwano sayo, yazisola njengobunengi bezisa zayo.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Yabanika izisa phambi kwabo bonke ababebathumbile.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sisindise, Nkosi Nkulunkulu wethu, usibuthe sivela ezizweni, ukubonga ibizo lakho elingcwele, ukuzincoma endumisweni yakho.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Kayibongwe iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli, kusukela phakade kuze kube sephakadeni! Abantu bonke kabathi: Ameni. Dumisani iNkosi!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Amahubo 106 >