< Amahubo 104 >

1 Bonga iNkosi, mphefumulo wami. Nkosi Nkulunkulu wami, umkhulu kakhulu; wembethe ubukhosi lodumo.
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 Ozembesa ngokukhanya njengesembatho, owendlala amazulu njengekhetheni.
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 Owabeka imijabo yamakamelo akhe aphezulu emanzini, owenza amayezi abe yinqola yakhe, ohamba phezu kwempiko zomoya.
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 Owenza izingilosi zakhe zibe yimimoya, izinceku zakhe zibe ngumlilo olamalangabi.
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 Wamisa umhlaba phezu kwezisekelo zawo, kawuyikuzanyazanyiswa phakade laphakade.
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 Wawugubuzela ngokujula njengesembatho; amanzi ema phezu kwezintaba.
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 Ekukhuzeni kwakho abaleka; elizwini lokuduma kwakho aphangisa asuka;
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 - zenyuka izintaba, zehla izihotsha - endaweni owawuwamisele wona.
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 Wamisa umngcele angewudlule, kawayikubuya agubuzele umhlaba.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 Othumela imithombo ezihotsheni, yahamba phakathi kwezintaba.
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 Yanathisa yonke inyamazana yeganga, obabhemi beganga bacitsha ukoma kwabo.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 Inyoni zamazulu zakhela emaceleni ayo, zizwakalisa ilizwi ziphakathi kwezingatsha.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 Uthelela izintaba esemakamelweni akhe aphezulu; umhlaba usuthiswa ngesithelo semisebenzi yakho.
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 Umilisela izifuyo utshani, lemibhida yokusiza umuntu, ukuveza ukudla emhlabathini,
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 lewayini elithokozisa inhliziyo yomuntu, ukwenza ubuso bukhanye ngamafutha, lesinkwa esiqinisa inhliziyo yomuntu.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 Ziyasutha izihlahla zeNkosi, imisedari yeLebhanoni eyayihlanyelayo.
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 Lapho inyoni ezakhela khona izidleke; ingabuzane, izihlahla zefiri ziyindlu yalo.
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 Intaba eziphakemeyo zingezamagogo, amadwala ayisiphephelo sezimbila.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 Inyanga wayenzela izikhathi ezimisiweyo; ilanga liyazi ukutshona kwalo.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 Wenza umnyama, kube sebusuku, phakathi kwabo kuphume yonke inyamazana yehlathi.
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 Izilwane ezintsha zibhongela impango, lokudinga ukudla kwazo kuNkulunkulu.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 Ilanga liphuma, zibuthane, zilale ezikhundleni zazo.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 Umuntu uphuma aye emsebenzini wakhe lemtshikatshikeni wakhe kuze kuhlwe.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 Minengi kangakanani imisebenzi yakho, Nkosi! Yonke uyenze ngenhlakanipho; umhlaba ugcwele inotho yakho.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 Lolulwandle olukhulu lolubanzi ngezinhlangothi, lapho okulezihuquzelayo khona ezingelakubalwa, izinto eziphilayo ezincinyane kanye lezinkulu.
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 Kuhamba khona imikhumbi, uLeviyathani owambumbela ukuthi adlale kulo.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 Zonke lezi zilindele kuwe, ukuthi uzinike ukudla kwazo ngesikhathi sazo.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 Uyazinika, zibuthe; uvula isandla sakho, zisuthe okuhle.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 Ufihla ubuso bakho, zikhathazeke; ususa umoya wazo, zife, zibuyele ethulini lwazo.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 Uthumela umoya wakho, zidalwe; wenze bube butsha ubuso bomhlaba.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 Udumo lweNkosi kalume kuze kube nininini; iNkosi kayithokoze ngemisebenzi yayo.
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 Ikhangela umhlaba, uthuthumele; ithinta izintaba, zithunqe.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 Ngizahlabelela iNkosi ngisaphila; ngizahlabelela indumiso kuNkulunkulu wami nxa ngisekhona.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 Ukuzindla kwami ngaye kuzakuba mnandi; mina ngizathokoza eNkosini.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Izoni kaziqedwe emhlabeni, kungabe kusaba khona ababi. Bonga iNkosi, mphefumulo wami. Dumisani iNkosi!
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.

< Amahubo 104 >