< Amahubo 10 >
1 Nkosi, umeleni khatshana? Ucatshelani ezikhathini zokuhlupheka?
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
2 Omubi ekuzigqajeni uyamzingelisisa umyanga; kababanjwe ngamagobe abawacebileyo.
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
3 Ngoba omubi uyazikhukhumeza ngesifiso somphefumulo wakhe, uyasibusisa isihwaba, ayeyise iNkosi.
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
4 Omubi, ngokuzigqaja kobuso bakhe uthi: Kakubizi; kakho uNkulunkulu emicabangweni yakhe yonke.
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
5 Indlela zakhe ziqinile isikhathi sonke; izahlulelo zakho ziphakeme zikhatshana laye; izitha zakhe zonke uyazivuthela.
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
6 Uthi enhliziyweni yakhe: Kangiyikunyikinywa; ngoba esizukulwaneni lesizukulwana kangiyikuba sebunzimeni.
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
7 Umlomo wakhe ugcwele ukuthuka lezinkohliso lobuqili; ngaphansi kolimi lwakhe kukhona ukona lobubi.
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
8 Uhlezi endaweni yokucathama yemizi, ezindaweni ezisithekileyo ubulala ongelacala; amehlo akhe akhangele othithibeleyo ngasese.
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
9 Uyacatsha ekusithekeni njengesilwane ebhalwini lwaso; ucatshela ukumbamba ongumyanga, uyabamba ongumyanga ngokumhudulela embuleni lakhe.
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
10 Uyaqutha, uyakhothama, njalo umyanga awe ngokulamandla kwakhe.
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
11 Uthi enhliziyweni yakhe: UNkulunkulu ukhohliwe, ufihle ubuso bakhe, kasoze abone lanini.
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
12 Sukuma, Nkosi! Nkulunkulu, phakamisa isandla sakho, ungabakhohlwa abahluphekayo.
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
13 Kungani omubi edelela uNkulunkulu? Uthi enhliziyweni yakhe: Kawuyikukubiza.
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
14 Uyabona, ngoba wena uyakhangela ububi lenhlupheko, ukukubeka esandleni sakho. Umyanga uyazinikela kuwe; wena ungumsizi wezintandane.
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
15 Yephula ingalo yokhohlakeleyo lomubi; dinga inkohlakalo yakhe ukuze ungabe usayithola.
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
16 UJehova yiNkosi kuze kube nini lanini; izizwe zibhubhile elizweni layo.
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
17 Nkosi, uzwile isifiso sabathobekileyo, uzaqinisa inhliziyo yabo, wenze indlebe yakho izwe,
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
18 ukwahlulela intandane locindezelweyo, ukuze umuntu wasemhlabeni angabe esesabeka.
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.