< Izaga 8 >
1 Inhlakanipho kayimemezi yini, lokuqedisisa kukhuphe ilizwi lakho?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Engqongeni yezindawo eziphakemeyo, ngasendleleni, phakathi kwezindlela kumi.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Eceleni kwamasango, entubeni yomuzi, ekungeneni kweminyango kuyamemeza kakhulu kuthi:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 Kini, madoda, ngiyamemeza, lelizwi lami lisebantwaneni babantu.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Lina elingelalwazi, qedisisani inhlakanipho; lani zithutha, qedisisani ngenhliziyo.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Zwanini, ngoba ngizakhuluma izinto zobukhosi, lokuvula kwendebe zami kuzakuba yikuqonda.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Ngoba umlomo wami ukhuluma iqiniso, lenkohlakalo iyisinengiso endebeni zami.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Wonke amazwi omlomo wami asekulungeni; kakukho okutshilekileyo lokugobileyo kuwo.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Wonke aqondile kulowo oqedisisayo, alungile kulabo abathola ulwazi.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Yemukelani ukufundisa kwami, hatshi isiliva, lolwazi kulegolide elikhethekileyo.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Ngoba inhlakanipho ingcono kulamatshe amahle, lakho konke okufisekayo kakulakulinganiswa layo.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Mina nhlakanipho ngihlala lokuqedisisa, ngithola ulwazi lamacebo.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Ukwesaba iNkosi kuyikuzonda ububi; ukuzigqaja, lokuziqhenya, lendlela embi, lomlomo wokuphambeka ngiyakuzonda.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Iseluleko ngesami, lenhlakanipho eqotho; ngiyikuqedisisa; amandla ngawami.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Ngami amakhosi ayabusa, lababusi bamisa ukulunga.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Ngami iziphathamandla ziyabusa, lezikhulu, bonke abehluleli bomhlaba.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Mina ngiyathanda abangithandayo, lalabo abangidingisisayo bazangithola.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Inotho lodumo kukimi, inotho eqhubekayo lokulunga.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Isithelo sami singcono kulegolide, legolide elicwengekileyo, lokutholakalayo kwami kulesiliva esikhethekileyo.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Ngihamba endleleni yokulunga, phakathi kwemikhondo yesahlulelo;
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 ukuthi ngenze abangithandayo badle ilifa lemfuyo; ngigcwalise iziphala zabo.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 INkosi, ngaba ngeyayo, ngaba yikuqala kwendlela yayo, ngaphambi kwemisebenzi yayo yendulo.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Ngamiswa kwasephakadeni, kusukela ekuqaleni, kusukela emandulo omhlaba.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Kungakabi khona izinziki ngasengizelwe, ingakabi khona imithombo enzima ngamanzi.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Intaba zingakamiswa, kungakabi khona amaqaqa, ngasengizelwe.
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Ingakawenzi umhlaba lemimango, lokuqala kwentuli zomhlaba.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Lapho ilungisa amazulu ngangikhonapho; lapho imisa umkhathi ngaphezu kwenziki;
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 lapho imisa amayezi ngaphezulu; lapho iqinisa imithombo yenziki;
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 lapho imisela ulwandle umngcele walo ukuze amanzi angeqi umlayo wayo; lapho imisa izisekelo zomhlaba;
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 khona ngangiseduze layo njengowakhuliswa yiyo, ngizintokozo zayo usuku ngosuku, ngithokoza phambi kwayo ngaso sonke isikhathi,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 ngidlala elizweni lomhlaba wayo, lentokozo zami zisebantwaneni babantu.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Ngakho-ke, bantwana bami, ngizweni; ngoba babusisiwe abagcina indlela zami.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Zwanini ukulaya, lihlakaniphe, lingakudeli.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Ubusisiwe umuntu ongizwayo, alinde insuku ngensuku emasangweni ami, alinde emigubazini yeminyango yami.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Ngoba ongitholayo uthola impilo, azuze umusa eNkosini.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Kodwa owona kimi wona umphefumulo wakhe; bonke abangizondayo bathanda ukufa.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”