< Izaga 31 >
1 Amazwi kaLemuweli inkosi yeMasa, unina amfundisa wona.
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 Ini, ndodana yami! Ini-ke, ndodana yesizalo sami! Ini-ke, ndodana yezithembiso zami!
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Unganiki amandla akho kwabesifazana, kumbe izindlela zakho ekubhubhiseni amakhosi.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 Kakusikwamakhosi, Lemuweli, kakusikwamakhosi ukunatha iwayini, kumbe okweziphathamandla ukuloyisa okunathwayo okulamandla.
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 Hlezi anathe, akhohlwe isimiso, aguqule isahlulelo sawo wonke amadodana enhlupheko.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Phana okunathwayo okulamandla kobhubhayo, lewayini kwabababayo emphefumulweni.
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 Kanathe, akhohlwe ubuyanga bakhe, angabe esakhumbula usizi lwakhe.
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Vulela isimungulu umlomo wakho, udaba lwabo bonke abamiselwe incithakalo.
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Vula umlomo wakho, wahlulele ngokulunga, umele ilungelo lomyanga loswelayo.
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 Ngubani ongathola umfazi okhuthela okulungileyo? Ngoba intengo yakhe iyedlula kakhulu amatshe amahle.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 Inhliziyo yomkakhe ithemba kuye, ukuze angasweli impango.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 Umenzela okuhle, hatshi okubi, insuku zonke zempilo yakhe.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 Udinga uboya bezimvu lefilakisi, asebenze ngenjabulo yezandla zakhe.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 Ufanana lemikhumbi yomthengisi; uletha ukudla kwakhe kuvela khatshana.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 Uvuka kusesebusuku, anike indlu yakhe ukudla, lesabelo kuzincekukazi zakhe.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 Anakane ngensimu ayizuze; ngesithelo sezandla zakhe ahlanyele ivini.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 Uyabhinca ukhalo lwakhe ngamandla, aqinise ingalo zakhe.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 Uyananzelela ukuthi ukuthengisa kwakhe kuhle; isibane sakhe kasicitshi ebusuku.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 Welulela izandla zakhe kuluthi lokuphotha, lezandla zakhe zibambe isigodo esilezintambo.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 Welulela umyanga isandla sakhe, elulele izandla zakhe koswelayo.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 Kesabi iliqhwa elikhithikileyo ngenxa yabendlu yakhe, ngoba bonke abendlu yakhe bagqokiswe okubomvu.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 Uzenzela izembeso; isigqoko sakhe sililembu elicolekileyo leliyibubende.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Umkakhe uyaziwa emasangweni, lapho ehlezi labadala belizwe.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 Wenza ilembu elicolekileyo kakhulu, alithengise; anike umthengi ibhanti.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 Amandla lodumo kuyisigqoko sakhe; uyahleka mayelana losuku olulandelayo.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 Uvula umlomo wakhe ngenhlakanipho; lemfundiso yomusa iselimini lwakhe.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 Uqaphela inhambo zomuzi wakhe; kadli isinkwa sobuvila.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 Abantwana bakhe bayavuka bathi ubusisiwe, lomkakhe laye uyamdumisa:
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 Manengi amadodakazi enze ngenkuthalo, kodwa wena wenyukile phezu kwawo wonke.
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Ubuhle buyinkohliso, lokubukeka kuyize; owesifazana owesaba iNkosi yena uzadunyiswa.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Mnikeni okuvela esithelweni sezandla zakhe, lemisebenzi yakhe kayimdumise emasangweni.
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.