< Izaga 23 >

1 Nxa uhlalela ukudla lesiphathamandla, qaphelisa lokuqaphelisa okuphambi kwakho.
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 Ubeke ingqamu emphinjeni wakho uba uyisiminzi.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Ungafisi izibondlo zaso, ngoba ziyikudla kwamanga.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Ungatshikatshikeli ukunotha; pheza ekuqedisiseni kwakho.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Uzandizisa yini amehlo akho kokungekho? Ngoba kuzazenzela lokuzenzela izimpiko njengokhozi oluphaphela emazulwini.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Ungadli ukudla kolelihlo elibi, ungafisi izibondlo zakhe.
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 Ngoba njengoba ecabangile emphefumulweni wakhe, unjalo. Uzakuthi: Dlana unathe; kodwa inhliziyo yakhe kayilawe.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Ucezu oludlileyo uzaluhlanza, wone amazwi akho amnandi.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Ungakhulumi endlebeni zoyisithutha, ngoba uzadelela inhlakanipho yamazwi akho.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Ungatshedisi isikhonkwane esidala somngcele; ungangeni emasimini ezintandane;
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 ngoba uMhlengi wazo ulamandla; yena uzamela udaba lwazo kuwe.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Beka inhliziyo yakho ekufundisweni, lezindlebe zakho emazwini olwazi.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Ungagodleli umntwana isijeziso; nxa umtshaya ngoswazi kayikufa.
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Wena uzamtshaya ngoswazi, ukhulule umphefumulo wakhe esihogweni. (Sheol h7585)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
15 Ndodana yami, uba inhliziyo yakho ihlakanipha, inhliziyo yami izathokoza, yebo eyami;
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 lezinso zami zizajabula ekukhulumeni kwendebe zakho izinto eziqondileyo.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Inhliziyo yakho kayingahawukeli izoni; kodwa bana ekwesabeni iNkosi lonke usuku.
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 Ngoba isibili kukhona umvuzo, lomlindelo wakho kawuyikuqunywa.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Lalela wena, ndodana yami, uhlakaniphe, uqondise inhliziyo yakho endleleni.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Ungabi phakathi kwabanathi bewayini, phakathi kwezihwaba zenyama.
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 Ngoba isidakwa lesihwaba sizakuba ngumyanga, lokuwozela kugqokisa amadabudabu.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Lalela uyihlo owakuzalayo, ungamdeleli unyoko esemdala.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Thenga iqiniso, ungalithengisi; inhlakanipho, lemfundiso, lokuqedisisa.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 Uyise wolungileyo uzathaba lokuthaba; lozala ohlakaniphileyo uzathokoza ngaye.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Uyihlo lonyoko kabathokoze, lokuzeleyo kathabe.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Ndodana yami, ngiphe inhliziyo yakho, lamehlo akho kawananzelele indlela zami.
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 Ngoba iwule lingumgodi otshonayo, lowesifazana owemzini ungumthombo ongumcingo.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 Laye ucathama njengomphangi, andise abangathembekanga phakathi kwabantu.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Ngubani olo: Maye? Ngubani olo: Wo? Ngubani olenkani? Ngubani olesililo? Ngubani olamanxeba ngeze? Ngubani olamehlo abomvu?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 Yilabo abalibala ewayinini, yilabo abazedinga iwayini elixutshanisiweyo.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Ungakhangeli iwayini, lapho lizibonakalisa libomvu, nxa linika umbala walo enkomitshini, lihamba liqondile.
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Ekucineni kwalo liluma njengenyoka, lilume njengebululu.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Amehlo akho azabona abesifazana bemzini, lenhliziyo yakho ikhulume izinto eziphambeneyo.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 Yebo, uzakuba njengolala enhliziyweni yolwandle, lanjengolala esihlokweni sensika yomkhumbi.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 Bangitshayile, kangizwanga buhlungu; bangidutshuzile, kangikunanzanga. Ngizavuka nini? Ngiphinde ngilidinge futhi.
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”

< Izaga 23 >