< Izaga 17 >

1 Ucezu olomileyo lokuthula kanye lalo lungcono kulendlu egcwele imihlatshelo lengxabano.
Gara ka ci busasshen burodi da kwanciyar rai kuma shiru da ka je cin abinci a gidan da ke cike da biki amma da ɓacin rai.
2 Inceku ehlakaniphileyo izabusa phezu kwendodana eyangisayo, yehlukanise ilifa phakathi kwezelamani.
Bawa mai hikima zai yi mulki a kan da mai rashin kunya, kuma zai raba gādo kamar ɗaya daga cikin’yan’uwansa.
3 Imbiza yokuncibilikisa ngeyesiliva, lesithando ngesegolide, kodwa iNkosi ihlola izinhliziyo.
Ana gwajin azurfa da kuma zinariya da wuta, amma Ubangiji ne mai gwajin zuciya.
4 Umenzi wobubi ulalela indebe ekhohlakeleyo; umqambimanga ubeka indlebe olimini oluchithayo.
Mugun mutum kan mai da hankali ga mugayen leɓuna; maƙaryaci yakan kasa kunne ga harshen ƙarairayi.
5 Oklolodela umyanga uthuka uMenzi wakhe; othokoza encithakalweni kayikuba msulwa.
Duk wanda yake wa matalauta ba’a yana zagin Mahaliccinsu ne; duk wanda ya yi murna akan masifar da ta sami wani za a hukunta shi.
6 Abantwana babantwana bangumqhele wabadala, lodumo lwabantwana ngoyise.
Jikoki rawanin tsofaffi ne, kuma iyaye su ne abin taƙamar’ya’yansu.
7 Indebe elobungcwethi kayisifanelanga isithutha; kakhulu kangakanani indebe yamanga isiphathamandla.
Leɓunan basira ba su dace da wawa ba, ya ma fi muni a ce mai mulki yana da leɓunan ƙarya!
8 Isipho siyilitshe eliligugu emehlweni abaniniso; loba ngaphi esiphendukela khona sizaphumelela.
Cin hanci kamar sihiri yake ga wanda yake ba da shi; ko’ina ya juye, yakan yi nasara.
9 Osibekela isiphambeko udinga uthando, kodwa ophindaphinda udaba wehlukanisa umngane oseduze.
Duk wanda ya rufe laifi yana inganta ƙauna ne, amma duk wanda ya yi ta maimaita batu yakan raba abokai na kusa.
10 Ukukhuza kuyajula koqedisisayo kulokutshaya isithutha ngokulikhulu.
Tsawata kan sa mutum ya koyi basira fiye da abin da wawa zai koya ko da an dūke shi sau ɗari.
11 Omubi udinga ububi kuphela, kodwa isithunywa esilesihluku sizathunyelwa kuye.
Mugayen mutane sukan kuta tawaye da Allah; za a aika manzo mutuwa a kansu.
12 Kakuthi ibhere elifelwe yimidlwane lihlangane lomuntu, kodwa hatshi isithutha ebuthutheni baso.
Gara a haɗu da beyar da aka ƙwace wa’ya’ya fiye da a sadu da wawa cikin wautarsa.
13 Ophindisela okubi esikhundleni sokuhle, ububi kabuyikusuka endlini yakhe.
In mutum ya sāka alheri da mugunta, mugunta ba za tă taɓa barin gidansa ba.
14 Ukuqala kwenkani kunjengokuvulela amanzi; ngakho yekela ingxabano ingakazivezi.
Farawar faɗa tana kamar ɓarkewa madatsar ruwa ne, saboda haka ka bar batun kafin faɗa ta ɓarke.
15 Olungisisa omubi lolahla olungileyo bayisinengiso eNkosini, ngitsho bobabili.
Baratar da mai laifi a kuma hukunta mai adalci, Ubangiji ya ƙi su biyu.
16 Kungani kulemali yokuthenga inhlakanipho esandleni sesithutha, lokhu singelangqondo?
Mene ne amfanin kuɗi a hannun wawa, da yake ba shi da sha’awar samun hikima?
17 Umngane uyathanda ngaso sonke isikhathi, lomzalwane uzalelwa inhlupheko.
Aboki yakan yi ƙauna a koyaushe, ɗan’uwa kuma, ai, don ɗaukar nawayar juna ne aka haife shi.
18 Umuntu oswela ingqondo uyabambana ngezandla ukuba yisibambiso phambi kukamakhelwane wakhe.
Mutumin da ba shi da azanci yakan ɗauki lamunin wani ya kuma ɗauki nauyin biyan basusuwan maƙwabci.
19 Othanda isiphambeko uthanda inkani; ophakamisa umnyango wakhe udinga ukubhujiswa.
Duk mai son faɗa yana son zunubi, duk wanda ya gina ƙofar shiga mai tsawo yana gayyatar hallaka.
20 Olenhliziyo ephambeneyo katholi okuhle, lophambene ngolimi uwela ebubini.
Mutum mai muguwar zuciya ba ya cin gaba; duk wanda yake da harshen ruɗu kan shiga wahala.
21 Ozala isithutha, sizakuba lusizi kuye; loyise wesithutha kathokozi.
Kasance da wawa kamar ɗa yakan kawo baƙin ciki babu farin ciki ga mahaifin wawa.
22 Inhliziyo ethokozayo yenza kuhle njengomuthi, kodwa umoya owephukileyo womisa amathambo.
Zuciya mai farin ciki magani ne mai kyau, amma bakin rai kan busar da ƙasusuwa.
23 Omubi uthatha isipho esifubeni ukuphambula izindlela zesahlulelo.
Mugun mutum yakan karɓa cin hanci a asirce don yă lalace yin adalci.
24 Inhlakanipho iphambi koqedisisayo, kodwa amehlo esithutha asekucineni komhlaba.
Mutum mai basira kan kafa idonsa a kan hikima, amma idanun wawa suna a kan ƙarshen duniya.
25 Indodana eyisiwula ilusizi kuyise, iyikubaba kowayizalayo.
Da yake wawa yakan kawo baƙin ciki ga mahaifinsa da ɓacin rai ga wanda ya haife shi.
26 Ukuhlawulisa olungileyo lakho kakulunganga, lokutshaya iziphathamandla ngenxa yobuqotho.
Ba shi da kyau a hukunta marar laifi, ko a bulale shugaba saboda mutuncinsu.
27 Owazi ulwazi ugodla amazwi akhe; umuntu oqedisisayo ulomoya opholileyo.
Mutum mai sani yakan yi la’akari da amfani da kalmomi, mutum mai basira kuma natsattse ne.
28 Isithutha esithuleyo laso sithiwa sihlakaniphile; ovala indebe zakhe uthiwa uyaqedisisa.
Ko wawa in bai buɗe bakinsa ba, za a zaci shi mai hikima ne, da kuma mai basira inda ya ƙame bakinsa.

< Izaga 17 >