< Izaga 1 >
1 Izaga zikaSolomoni, indodana kaDavida, inkosi yakoIsrayeli;
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 ukwazi inhlakanipho lokulaywa, ukuqedisisa amazwi okuqedisisa,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 ukwemukela ukulaya kwenhlakanipho, ukulunga, lesahlulelo, lokuqonda;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 ukunika abangelalwazi inhlakanipho, ijaha ulwazi lengqondo.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Ohlakaniphileyo uzakuzwa, andise ukufunda, loqedisisayo uzazuza izeluleko,
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 ukuqedisisa isaga lomzekeliso, amazwi abahlakaniphileyo, lamalibho abo.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 Ukwesaba iNkosi kuyikuqala kolwazi; izithutha ziyadelela inhlakanipho lokulaywa.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Ndodana yami, zwana ukulaya kukayihlo, ungawudeli umlayo kanyoko;
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 ngoba kuzakuba ngumqhele womusa ekhanda lakho, lemigaxo entanyeni yakho.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Ndodana yami, uba izoni zikuhuga, ungavumi.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Uba zisithi: Hamba lathi, siyecathamela igazi, sicatshele ongelacala kungelasizatho;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 sibaginye bephila njengengcwaba, yebo, ngokupheleleyo, njengabehlela egodini. (Sheol )
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
13 Sizathola yonke impahla eligugu, sigcwalise izindlu zethu ngempango.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Phosela inkatho yakho phakathi kwethu; sonke sibe lesikhwama semali sinye.
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Ndodana yami, ungahambi lazo endleleni; unqande unyawo lwakho emkhondweni wazo.
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Ngoba inyawo zazo zigijimela ebubini, ziphangisa ukuchitha igazi.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Isibili, imbule lendlalelwa ize phambi kwamehlo aloba yiyiphi inyoni.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Lalaba bacathamela igazi labo, bacatshele imiphefumulo yabo.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Zinjalo indlela zakhe wonke ozuza inzuzo ngokuphanga; ithatha impilo yabaniniyo.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 UkuHlakanipha kuyamemeza ngaphandle, kukhupha ilizwi lakho emidangeni.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 Kuyamemeza endaweni eqakathekileyo yokuxokozela, ekungeneni kwamasango; emzini kutsho amazwi akho,
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 kusithi: Koze kube nini, lina elingelalwazi, lithanda ukungabi lalwazi, labaklolodayo bezifisela ukukloloda, leziphukuphuku zizonda ulwazi?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Phendukelani ekukhuzeni kwami; khangelani, ngizathululela umoya wami kini, ngilazise amazwi ami.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Ngoba ngibizile, kodwa lala; ngelulile isandla sami, kodwa kakho onanzayo;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 ladelela sonke iseluleko sami, kalivumanga ukukhuza kwami;
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 mina-ke ngizahleka ukuchitheka kwenu, ngiklolode ekufikeni kokwesaba kwenu,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 ekufikeni kokwesaba kwenu njengesiphepho, lokuchitheka kwenu kufika njengesivunguzane, lapho ubuhlungu losizi kulehlela.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Khona bazangibiza, kodwa kangiyikusabela; bazangidingisisa, kodwa kabayikungithola.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Ngenxa yokuthi babezonda ulwazi, bengakhethanga ukwesaba iNkosi.
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 Kabavumanga iseluleko sami, bedelela konke ukukhuza kwami.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Ngakho bazakudla okwesithelo sendlela yabo, basuthiswe ngamacebo abo.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Ngoba ukuhlehla kwabangelalwazi kuzababulala, lokonwaba kweziphukuphuku kuzababhubhisa.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Kodwa ongilalelayo uzahlala evikelekile, onwabe ekwesabeni okubi.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”