< UFilimoni 1 >

1 UPawuli isibotshwa sikaKristu Jesu loTimothi umzalwane, kuFilimoni othandekayo lesisebenzi kanye lathi,
Bulus, ɗan kurkuku saboda Kiristi Yesu, da kuma Timoti ɗan’uwanmu, Zuwa ga Filemon ƙaunataccen abokinmu da kuma abokin aikinmu,
2 lakuApifiya othandekayo, lakuArkipho owebutho kanye lathi, lakubandla elisendlini yakho:
zuwa kuma ga Affiya’yar’uwarmu, zuwa kuma ga Arkiffus abokin famarmu, da zuwa kuma ga ikkilisiyar da take taruwa a gidanka.
3 Umusa kawube kini lokuthula okuvela kuNkulunkulu uBaba wethu leNkosini uJesu Kristu.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 Ngiyambonga uNkulunkulu wami, ngikuphatha ngezikhathi zonke emikhulekweni yami,
Kullum nakan gode wa Allahna sa’ad da nake tuna da kai cikin addu’o’ina,
5 ngisizwa ngothando lwakho langokholo olalo eNkosini uJesu lakubo bonke abangcwele,
domin ina jin labari bangaskiyarka cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunarka da kake yi saboda dukan tsarkaka.
6 ukuze ukuhlanganyela kokholo lwakho kube lamandla elwazini lwento yonke enhle ekini kuKristu Jesu.
Ina addu’a ka zama mai ƙwazo cikin shaida bangaskiyarka, domin ka sami cikakken fahimta ta kowane abin da yake nagarin da muke da shi cikin Kiristi.
7 Ngoba silentokozo enkulu lenduduzo ethandweni lwakho, ngoba imibilini yabangcwele yavuselelwa ngawe, mzalwane.
Ƙaunarka ta sa ni farin ciki ƙwarai ta kuma ƙarfafa ni, domin kai, ɗan’uwa, ka wartsake zukatan tsarkaka.
8 Ngalokho, lanxa ngilesibindi esikhulu kuKristu sokuthi ngikulaye into efaneleyo,
Saboda haka, ko da yake cikin Kiristi ina iya yin ƙarfin hali in umarce ka ka yi abin da ya kamata,
9 kanti ngenxa yothando kungcono ukuthi ngincenge, nginjengonje, uPawuli omdala, esengiyisibotshwa futhi sikaJesu Kristu.
duk da haka ina roƙonka saboda ƙauna, na fi so in roƙe ka, ni Bulus tsoho, a yanzu kuma ga ni ɗan sarƙa saboda Kiristi Yesu.
10 Ngiyakuncenga ngomntanami, engimzeleyo kuzibopho zami, uOnesimo,
Ina roƙonka saboda ɗana Onesimus, wanda ya zama ɗana yayinda nake cikin sarƙoƙi.
11 okade engelasizo kuwe, kodwa khathesi-ke ulosizo kuwe lakimi,
Dā kam, ba shi da amfani a gare ka, amma yanzu ya zama da amfani a gare ka da kuma gare ni.
12 engimbuyisela kuwe; kodwa wena, memukele, okuyikuthi imibilini yami;
Ina aike shi yă koma gare ka, shi da yake zuciyata.
13 ebengifisa mina ukumbamba abe lami, ukuze angisebenzele esikhundleni sakho kuzibopho zevangeli;
Na so in riƙe shi a wurina a madadinka domin yă taimake ni yayinda nake cikin sarƙoƙi saboda bishara.
14 kodwa kangithandanga ukwenza ulutho ngaphandle kwemvumo yakho, ukuze okuhle kwakho kungabi ngokokubanjwa ngamandla, kodwa njengokwesihle.
Sai dai ban so in yi kome ban da yardarka ba, domin kowane alherin da za ka yi, yă fito daga zuciyarka, ba na tilas ba.
15 Ngoba mhlawumbe wehlukaniswa lawe okwesikhatshana ngenxa yalokhu, ukuze ubuye umemukele phakade; (aiōnios g166)
Wataƙila abin da ya sa aka raba ka da shi na ɗan lokaci ƙanƙani shi ne don ka same shi da amfani (aiōnios g166)
16 angabe esaba njengesigqili, kodwa ngaphezu kwesigqili, umzalwane othandekayo, ikakhulu kimi, kodwa kakhulu kangakanani kuwe konke enyameni leNkosini.
ba kamar bawa kuma ba, sai dai fiye da bawa, a matsayin ƙaunataccen ɗan’uwa. Shi ƙaunatacce ne sosai a gare ni amma a gare ka ya ma fi zama ƙaunatacce, kamar mutum da kuma kamar ɗan’uwa a cikin Ubangiji.
17 Ngakho uba usithi ngingumhlanganyeli lawe, memukele njengami.
Saboda haka in ka ɗauke ni a kan ni abokin tarayya ne, sai ka marabce shi kamar yadda za ka marabce ni.
18 Kodwa uba ekone ngolutho kumbe elomlandu, lokho kubalele kimi;
In ya yi maka wani laifi ko kuma yana riƙe maka wani bashi, sai ka mai da shi a kaina.
19 mina Pawuli ngibhale ngesandla sami, mina ngizahlawula; ukuthi ngingatsho kuwe ukuthi lawe uqobo ulomlandu oseleyo kimi.
Ni, Bulus, nake rubuta wannan da hannuna. Zan biya ka, kada ma a yi zancen ranka da kake riƙe mini bashi.
20 Yebo, mzalwane, sengathi ngingaba lentokozo ngawe eNkosini; uvuselele imibilini yami eNkosini.
Ina fata, ɗan’uwa, zan sami amfani daga gare ka cikin Ubangiji; ka wartsake zuciyata cikin Kiristi.
21 Ngikubhalele ngithemba ukulalela kwakho, ngisazi ukuthi lawe uzakwenza okungaphezu kwalokho engikutshoyo.
Da tabbacin biyayyarka, ina rubuta maka, da sanin za ka yi fiye da abin da na ce.
22 Futhi ngesikhathi esifananayo ungilungisele lami indawo yokuhlala; ngoba ngiyathemba ukuthi ngemikhuleko yenu ngizanikwa kini.
Abu guda ya rage, ka shirya mini masauƙi, domin ina bege za a mayar da ni gare ku albarkacin addu’o’inku.
23 Uyakubingelela uEpafra oyisibotshwa kanye lami kuKristu Jesu,
Efafaras, abokin tarayyata a kurkuku cikin Kiristi Yesu, yana gaishe ka.
24 uMarko, uAristako, uDema, uLuka, izisebenzi kanye lami.
Haka kuma Markus, Aristarkus, Demas da kuma Luka, abokan aikina.
25 Umusa weNkosi yethu uJesu Kristu kawube lomoya wenu. Ameni.
Alherin Ubangiji Yesu Kiristi yă kasance da ruhunku.

< UFilimoni 1 >