< Amanani 32 >
1 Mayelana labantwana bakoRubeni labantwana bakoGadi, babelenkomo ezinengi, ezinengi kakhulu. Sebebone ilizwe leJazeri lelizwe leGileyadi, khangela-ke, indawo yayiyindawo yenkomo.
Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
2 Ngakho abantwana bakoGadi labantwana bakoRubeni beza bakhuluma kuMozisi lakuEleyazare umpristi lakuziphathamandla zenhlangano, besithi:
Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
3 IAtarothi leDiboni leJazeri leNimra leHeshiboni leEleyale leSebamu leNebo leBeyoni,
“Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
4 ilizwe iNkosi eyalitshayayo phambi kwenhlangano yakoIsrayeli, liyilizwe lezinkomo; futhi izinceku zenu zilezinkomo.
ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
5 Basebesithi: Nxa sithole umusa emehlweni akho, ilizwe leli kaliphiwe inceku zakho libe yimfuyo; ungasichaphisi iJordani.
Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
6 UMozisi wasesithi ebantwaneni bakoGadi lebantwaneni bakoRubeni: Abafowenu bazakuya empini, lina-ke lihlale lapha yini?
Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
7 Njalo lizadaniselani inhliziyo yabantwana bakoIsrayeli ukuze bangachaphi ukuya elizweni iNkosi ebanike lona?
Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
8 Benza njalo oyihlo mhla ngibathuma besuka eKadeshi-Bhaneya ukubona ilizwe.
Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
9 Ekuhambeni kwabo ukuya esihotsheni seEshikoli, balibona ilizwe, badanisa inhliziyo yabantwana bakoIsrayeli ukuze bangangeni elizweni iNkosi eyayibanike lona.
Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
10 Ulaka lweNkosi lwaseluvutha ngalolusuku, yasifunga isithi:
A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
11 Isibili kakho kumadoda enyuka esuka eGibhithe, kusukela koleminyaka engamatshumi amabili langaphezulu ozalibona ilizwe engalifungela uAbrahama, uIsaka loJakobe, ngoba kabangilandelanga ngokupheleleyo;
‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
12 ngaphandle kukaKalebi indodana kaJefune umKenizi, loJoshuwa indodana kaNuni, ngoba balandele iNkosi ngokupheleleyo.
ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
13 Lolaka lweNkosi lwamvuthela uIsrayeli, yasibazulisa enkangala iminyaka engamatshumi amane, kwaze kwaphela isizukulwana sonke esasenze okubi emehlweni eNkosi.
Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
14 Khangelani-ke, selivukile esikhundleni saboyihlo, inzalo yabantu abonayo, ukwandisa futhi intukuthelo yeNkosi evuthela uIsrayeli.
“Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
15 Uba liphenduka ekuyilandeleni, izaphinda njalo ibatshiye enkangala; njalo lizabhubhisa bonke lababantu.
In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
16 Basebesondela kuye bathi: Sizakwakha lapha izibaya zezifuyo zethu, lemizi yabantwanyana bethu;
Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
17 kodwa thina sizahloma silungile phambi kwabantwana bakoIsrayeli, size sibafikise endaweni yabo, labantwanyana bethu bazahlala emizini evikelekileyo, ngenxa yabahlali belizwe.
Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
18 Kasiyikubuyela emizini yethu, abantwana bakoIsrayeli baze badle, ngulowo lalowo ilifa lakhe.
Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
19 Ngoba kasiyikudla ilifa kanye labo ngaphetsheya kweJordani langaphambili, ngoba ilifa lethu selehlele kithi nganeno kweJordani empumalanga.
Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
20 UMozisi wasesithi kubo: Nxa lisenza linto, nxa lizahamba lihlomele impi phambi kweNkosi,
Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
21 beselichapha iJordani, wonke ohlomileyo kini, phambi kweNkosi, ize ixotshe izitha zayo phambi kwayo,
in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
22 lelizwe lehliselwe phansi phambi kweNkosi, khona emva kwalokho lizabuya, lingabi lacala eNkosini lakuIsrayeli; lalelilizwe lizakuba yilifa lenu phambi kweNkosi.
to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
23 Kodwa nxa lingenzi njalo, khangelani lizabe lonile eNkosini; ngakho yazini ukuthi isono senu sizalithola.
“Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
24 Zakheleni imizi yabantwanyana benu lezibaya zezimvu zenu, njalo yenzani lokho okuphume emlonyeni wenu.
Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
25 Abantwana bakoGadi labantwana bakoRubeni basebekhuluma kuMozisi besithi: Izinceku zakho zizakwenza njengalokho inkosi yami ilaya.
Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
26 Abantwanyana bethu, omkethu, izimvu zethu, lazo zonke izifuyo zethu kuzakuba lapho emizini yeGileyadi;
’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
27 kodwa inceku zakho zizachapha, ngulowo lalowo ehlomele impi, phambi kukaJehova empini, njengokutsho kwenkosi yami.
Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
28 UMozisi waselayezela ngabo kuEleyazare umpristi, loJoshuwa indodana kaNuni, lenhloko zaboyise zezizwe zabantwana bakoIsrayeli.
Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
29 UMozisi wasesithi kubo: Nxa abantwana bakoGadi labantwana bakoRubeni bechapha lani iJordani, wonke ehlomele impi, phambi kweNkosi, lelizwe lisehliselwa phansi phambi kwenu, khona lizabanika ilizwe leGileyadi libe yimfuyo.
ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
30 Kodwa uba bengachaphi lani behlomile, bazakuba lemfuyo phakathi kwenu elizweni leKhanani.
Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
31 Abantwana bakoGadi labantwana bakoRubeni basebephendula besithi: Lokhu iNkosi esikutshilo kunceku zakho - sizakwenza njalo.
Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
32 Thina sizachapha sihlomile phambi kweNkosi siye elizweni leKhanani, ukuze imfuyo yelifa lethu ibe ngeyethu nganeno kweJordani.
Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
33 Njalo uMozisi wabanika, kubantwana bakoGadi lakubantwana bakoRubeni lakungxenye yesizwe sakoManase, indodana kaJosefa, umbuso kaSihoni inkosi yamaAmori, lombuso kaOgi inkosi yeBashani, ilizwe lemizi yalo emingceleni, imizi yelizwe inhlangothi zonke.
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34 Labantwana bakoGadi bakha iDiboni leAtarothi leAroweri
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35 leAtirothi-Shofani leJazeri leJogibeha,
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36 leBeti-Nimra leBeti-Harani, imizi evikelweyo, lezibaya zezimvu.
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37 Labantwana bakoRubeni bakha iHeshiboni leEleyale leKiriyathayimi
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38 leNebo leBhali-Meyoni (sekuguqulwe amabizo) leSibima; basebebiza amabizo emizi abayakhayo ngamanye amabizo.
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
39 Labantwana bakoMakiri indodana kaManase baya eGileyadi, bayithumba, bawakhupha amaAmori emfuyweni yawo ayekuyo.
Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
40 UMozisi wasenika uMakiri indodana kaManase iGileyadi, wasehlala kiyo.
Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
41 LoJayiri indodana kaManase wayathumba imizana yayo, wayibiza ngokuthi yiHavothi-Jayiri.
Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
42 LoNoba wayathumba iKenathi, lemizana yayo, wayibiza ngokuthi yiNoba ngebizo lakhe.
Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.