< Amanani 16 >
1 UKora indodana kaIzihari indodana kaKohathi indodana kaLevi, loDathani loAbiramu amadodana kaEliyabi, loOni indodana kaPelethi, amadodana kaRubeni, basebethatha amadoda.
Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
2 Basebesukuma phambi kukaMozisi, lamadoda abantwana bakoIsrayeli, abangamakhulu amabili lamatshumi amahlanu, abangabakhokheli benhlangano, abakhethiweyo bomhlangano, amadoda alebizo.
suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
3 Bahlangana bamelana loMozisi bamelana loAroni, bathi kubo: Seledlulise amalawulo! Ngoba inhlangano yonke, bonke bangcwele, leNkosi iphakathi kwabo. Pho, liziphakamiselani phezu kwebandla leNkosi?
tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
4 Kwathi uMozisi esekuzwile, wathi mbo ngobuso bakhe phansi.
Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
5 Wasekhuluma kuKora lakuqembu lakhe lonke esithi: Kusisa, khona iNkosi izatshengisa ukuthi ngubani ongowayo lokuthi ngubani ongcwele, izamsondeza kuyo, lalowo emkhethileyo izamsondeza kuyo.
Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
6 Yenzani lokhu: Zithatheleni imiganu yokutshisela impepha, uKora, leqembu lakhe lonke,
Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
7 lifake kiyo umlilo, libeke kiyo impepha phambi kweNkosi kusasa. Kuzakuthi indoda iNkosi eyikhethayo, yiyo engcwele. Seledlulise amalawulo, madodana kaLevi!
ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
8 UMozisi wasesithi kuKora: Ake lizwe, madodana kaLevi;
Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
9 kuyinto encinyane kini yini ukuthi uNkulunkulu kaIsrayeli ulehlukanisile lenhlangano yakoIsrayeli ukuze alisondeze kuye ukuthi lenze inkonzo yethabhanekele leNkosi, lokuthi lime phambi kwenhlangano ukubakhonza?
Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
10 Ukusondezile, labafowenu bonke, amadodana kaLevi, kanye lawe; selifuna lobupristi yini?
Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
11 Ngalokho wena leqembu lakho lonke selihlangene ukumelana leNkosi. Ngoba uAroni uyini ukuthi limngungunele?
Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
12 UMozisi wasethuma ukubiza uDathani loAbiramu, amadodana kaEliyabi. Kodwa bathi: Kasiyikwenyuka;
Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
13 kuyinto encinyane yini ukuthi wasenyusa sivela elizweni eligeleza uchago loluju ukusibulala enkangala, kanti lawe usuzenza umbusi phezu kwethu?
Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
14 Futhi kawusingenisanga elizweni eligeleza uchago loluju, loba ukusinika ilifa lamasimu lezivini. Amehlo ala amadoda ungawakopola yini? Asiyikwenyuka.
Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
15 UMozisi wasethukuthela kakhulu, wathi eNkosini: Unganaki umnikelo wabo. Kangithathanga ubabhemi oyedwa wabo, futhi kangenzanga okubi komunye wabo.
Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
16 UMozisi wasesithi kuKora: Wena leqembu lakho lonke banini phambi kweNkosi, wena, labo, loAroni, kusasa;
Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
17 thathani, omunye lomunye umganu wakhe wokutshisela impepha, lifake kuyo impepha, liyisondeze phambi kweNkosi, kube ngulowo lalowo umganu wakhe wokutshisela impepha, imiganu yokutshisela impepha engamakhulu amabili lamatshumi amahlanu; lawe loAroni, ngulowo lalowo umganu wakhe wokutshisela impepha.
Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
18 Basebethatha, ngulowo lalowo umganu wakhe wokutshisela impepha, bafaka umlilo kuyo, babeka impepha kuyo, bema emnyango wethente lenhlangano, loMozisi loAroni.
Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
19 UKora wasebuthanisa inhlangano yonke ukumelana labo emnyango wethente lenhlangano. Inkazimulo yeNkosi yasibonakala ebandleni lonke.
Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
20 INkosi yasikhuluma kuMozisi lakuAroni isithi:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
21 Zehlukaniseni liphume phakathi kwalinhlangano ukuze ngibaqede ngokucwayiza kwelihlo.
“Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
22 Basebesithi mbo ngobuso babo phansi bathi: Nkulunkulu, Nkulunkulu wemimoya yayo yonke inyama, kona umuntu oyedwa, ubusuthukuthelela inhlangano yonke yini?
Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
23 INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
24 Tshono enhlanganweni uthi: Yenyukani lisuke kunhlangothi zonke zomuzi kaKora, uDathani, loAbiramu.
“Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
25 UMozisi wasesukuma, waya kuDathani loAbiramu, labadala bakoIsrayeli bamlandela.
Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
26 Wasekhuluma enhlanganweni esithi: Ake lisuke emathenteni alamadoda amabi, lingathinti lutho olungolwabo, hlezi liphetshulwe ezonweni zabo zonke.
Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
27 Basebesenyuka besuka emzini yaboKora, uDathani loAbiramu enhlangothini zonke; oDathani loAbiramu basebephuma, bema emnyango wamathente abo labomkabo lamadodana abo labantwanyana babo.
Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
28 UMozisi wasesithi: Ngalokhu lizakwazi ukuthi iNkosi ingithumile ukwenza yonke limisebenzi, lokuthi kakusikho okwengqondo yami.
Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
29 Uba laba besifa njengokufa kwabantu bonke, kumbe behlelwe njengokwehlelwa kwabantu bonke, iNkosi kayingithumanga.
In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
30 Kodwa uba iNkosi idala into entsha, ukuthi umhlaba uvule umlomo wawo, ubaginye lakho konke okwabo, behlele emgodini bephila, lizaqedisisa ukuthi lamadoda ayidelele iNkosi. (Sheol )
Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
31 Kwasekusithi eseqedile ukukhuluma wonke la amazwi, umhlaba owawungaphansi kwabo waqhekezeka,
Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
32 lomhlaba wavula umlomo wawo, wabaginya lezindlu zabo, labo bonke abantu ababengabakaKora, lempahla yabo yonke.
ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
33 Basebetshona emgodini bephila bona lakho konke okwabo; umhlaba wabagqibela, babhubha besuka phakathi kwebandla. (Sheol )
Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
34 UIsrayeli wonke owayebazingelezele wasebaleka ekukhaleni kwabo, ngoba bathi: Hlezi umhlaba usiginye.
Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
35 Kwasekuphuma umlilo eNkosini, waqothula amadoda angamakhulu amabili lamatshumi amahlanu ayenikele impepha.
Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
36 INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
Ubangiji ya ce wa Musa,
37 Tshono kuEleyazare, indodana kaAroni umpristi, ukuthi athathe imiganu yokutshisela impepha phakathi kokutsha; uwuchithachithele umlilo laphayana, ngoba ingcwele.
“Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
38 Imiganu yokutshisela impepha yalezizoni imelene lemiphefumulo yazo, kabayenze ibe yizicecedu ezibanzi zibe yisisibekelo selathi; ngoba bayinikele phambi kweNkosi, ngakho ingcwele; njalo izakuba yisibonakaliso ebantwaneni bakoIsrayeli.
gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
39 UEleyazare umpristi wasethatha imiganu yethusi yokutshisela impepha ababenikele ngayo abatshisiweyo, basebeyikhanda yaba yizicecedu zokusibekela ilathi,
Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
40 kube yisikhumbuzo ebantwaneni bakoIsrayeli ukuze kungabi lowemzini, ongesuye owenzalo kaAroni, osondela ukutshisa impepha phambi kweNkosi, ukuze angabi njengoKora lanjengexuku lakhe, njengoba iNkosi yakhuluma kuye ngesandla sikaMozisi.
yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
41 Kodwa kusisa inhlangano yonke yabantwana bakoIsrayeli yabasola oMozisi loAroni, isithi: Lina libabulele abantu beNkosi.
Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
42 Kwasekusithi inhlangano isihlangene imelene loMozisi njalo imelene loAroni, baphendukela ethenteni lenhlangano, khangela-ke iyezi lalilisibekele lenkazimulo yeNkosi yabonakala.
Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
43 UMozisi loAroni basebesiza ngaphambi kwethente lenhlangano.
Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
44 INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
45 Yenyukani lisuke phakathi kwalinhlangano, ukuze ngibaqede njengokucwayiza kwelihlo. Basebesithi mbo ngobuso babo phansi.
“Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
46 UMozisi wasesithi kuAroni: Thatha umganu wokutshisela impepha, ufake kuwo umlilo ovela elathini, ubeke kuwo impepha, uye ngokuphangisa enhlanganweni, ubenzele inhlawulo yokuthula; ngoba ulaka seluphumile lusuka phambi kweNkosi, inhlupheko isiqalisile.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
47 UAroni wasekuthatha njengokutsho kukaMozisi, wagijimela phakathi kwebandla, khangela-ke, inhlupheko yayisiqalisile phakathi kwabantu. Wafaka impepha, wabenzela abantu inhlawulo yokuthula.
Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
48 Wasesima phakathi kwabafileyo labaphilayo. Inhlupheko yasimiswa.
Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
49 Labafayo enhluphekweni babeyizinkulungwane ezilitshumi lane lamakhulu ayisikhombisa, ngaphandle kwalabo abafa ngendaba kaKora.
Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
50 UAroni wasebuyela kuMozisi emnyango wethente lenhlangano; lenhlupheko yayisimisiwe.
Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.