< UNehemiya 9 >

1 Ngosuku lwamatshumi amabili lane lwaleyonyanga abantwana bakoIsrayeli basebebuthana ngokuzila ukudla, langamasaka, lenhlabathi phezu kwabo.
A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, Isra’ilawa suka taru, suna yin azumi, suna sa rigunan makoki, suna kuma zuba toka a kansu.
2 Inzalo yakoIsrayeli yasizehlukanisa labo bonke abezizweni; basebesima bavuma izono zabo lobubi baboyise.
Waɗanda suke zuriyar Isra’ilawa suka ware kansu daga dukan baƙi. Suka tsaya, suka kuma furta zunubansu da muguntar kakanninsu.
3 Basebesukuma endaweni yabo yokuma, bafunda egwalweni lomlayo weNkosi uNkulunkulu wabo ingxenye yesine yosuku; njalo ngengxenye yesine bavuma futhi bakhonza iNkosi uNkulunkulu wabo.
Sa’ad da suke nan a tsaye, aka ɗauki awa uku ana karanta Littafin Dokar Ubangiji Allahnsu. Aka kuma ɗauki awa uku ana sujada ga Ubangiji Allahnsu.
4 Lezikhwelweni zamaLevi kwakumi oJeshuwa, loBani, uKadimiyeli, uShebaniya, uBuni, uSherebiya, uBani, uKenani; bamemeza ngelizwi elikhulu eNkosini uNkulunkulu wabo.
A kan dakalin kuwa akwai Lawiyawa, wato, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani da Kenani tsaye, waɗanda suka kira da babbar murya ga Ubangiji Allahnsu.
5 AmaLevi, oJeshuwa, loKadimiyeli, uBani, uHashabineya, uSherebiya, uHodiya, uShebaniya, uPethahiya basebesithi: Sukumani libusise iNkosi uNkulunkulu wenu kusukela ephakadeni kuze kube nininini; kalibusiswe ibizo lakho elilodumo eliphakanyiswe phezu kwaso sonke isibusiso lendumiso.
Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
6 Nguwe oyiNkosi wena wedwa, wena wenza amazulu, izulu lamazulu lalo lonke ibutho lawo, umhlaba lakho konke okukuwo, izinlwandle lakho konke okukuzo, wena uyagcina konke kuphila; lebutho lamazulu liyakukhonza.
Kai kaɗai ne Ubangiji. Kai ka yi sammai, har ma da sama sammai, da dukan rundunar taurari, da duniya da kuma dukan abin da yake cikinta, da tekuna da dukan abubuwan da suke cikinsu. Ka ba da rai ga kome, kuma rundunonin sama suna maka sujada.
7 Wena uyiNkosi uNkulunkulu, owakhetha uAbrama wamkhupha eUri yamaKhaladiya, wenza ibizo lakhe laba nguAbrahama;
“Kai ne Ubangiji Allah, wanda ya zaɓi Abram, ya fitar da shi daga Ur na Kaldiyawa, ya kuma ba shi suna Ibrahim.
8 wafica inhliziyo yakhe ithembekile phambi kwakho, wenza laye isivumelwano sokunika ilizwe lamaKhanani, amaHethi, amaAmori, lamaPerizi, lamaJebusi, lamaGirigashi, ukulinika inzalo yakhe; uwamisile amazwi akho, ngoba ulungile.
Kai ka sami zuciyarsa da aminci a gare ka, ka kuma yi alkawari da shi cewa za ka ba zuriyarsa ƙasar Kan’aniyawa, da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, da ta Yebusiyawa, da kuma ta Girgashiyawa. Ka kiyaye alkawarinka domin kai mai adalci ne.
9 Wabona ukuhlupheka kwabobaba eGibhithe, wezwa ukukhala kwabo ngasoLwandle oluBomvu,
“Ka ga wahalar kakanninmu a Masar; ka kuwa ji kukansu a Jan Teku.
10 wenza izibonakaliso lezimangaliso kuFaro lakuzo zonke inceku zakhe lakubo bonke abantu belizwe lakhe, ngoba wazi ukuthi baziphatha ngokuzigqaja kubo; njalo wazenzela ibizo njengalamuhla.
Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
11 Wehlukanisa ulwandle phambi kwabo ukuze bachaphe phakathi kolwandle emhlabathini owomileyo; wasuphosela ababaxotshayo ezinzikini njengelitshe emanzini alamandla.
Ka raba teku a gaban kakanninmu, saboda su wuce cikinsa a busasshiyar ƙasa, amma ka hallaka masu binsu cikin zurfafa, nutse kamar dutse a cikin ruwa.
12 Wasubakhokhela ngensika yeyezi emini langensika yomlilo ebusuku ukubakhanyisela indlela abazahamba ngayo.
Da rana ka bishe kakanninmu da girgije, da dare kuwa ka bishe su da ginshiƙin wuta don ka ba su haske a hanyar da za su bi.
13 Wehlela phezu kwentaba yeSinayi, wakhuluma labo usemazulwini, wabanika izahlulelo eziqondileyo, lemilayo eqotho, izimiso lemilayezelo elungileyo,
“Ka sauko a kan Dutsen Sinai; ka yi musu magana daga sama. Ka ba su ƙa’idodi da dokokin da suke masu adalci da kuma daidai, ka ba su farillai da umarnai da suke da kyau.
14 wabazisa isabatha lakho elingcwele, wabalaya imilayo, lezimiso, lomthetho, ngesandla sikaMozisi inceku yakho.
Ka sanar da su Asabbacinka mai tsarki, ka kuma ba su umarnai, da farillai, da kuma dokoki ta wurin bawanka Musa.
15 Wabanika isinkwa esivela emazulwini ekulambeni kwabo, lamanzi edwaleni wabakhuphela wona ekomeni kwabo; wabatshela ukuthi bazangena badle ilifa lelizwe owaphakamisa isandla sakho ukubanika lona.
Cikin yunwansu ka ba su burodi daga sama, cikin ƙishirwansu kuma ka fitar musu ruwa daga dutse. Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka rantse ta wurin ɗaga hannu cewa za ka ba su.
16 Kodwa bona labobaba baziphatha ngokuzigqaja, benza lukhuni intamo yabo, kabayilalelanga imilayo yakho.
“Amma su kakanninmu, suka yi fariya da taurinkai, ba su kuwa yi biyayya ga umarnanka ba.
17 Yebo, bala ukulalela, kabakhumbulanga izimangaliso zakho owazenza kubo; kodwa bazenza lukhuni intamo yabo, lekuvukeleni kwabo bamisa induna ukuze babuyele ebugqilini babo. Kodwa wena unguNkulunkulu wezintethelelo, olomusa, lesihawu, ophuza ukuthukuthela, lowande ngothando, kawubatshiyanga.
Suka ƙi su saurare ka, suka kāsa tuna da mu’ujizan da ka aikata a cikinsu. Suka yi taurinkai, cikin tawayensu kuma suka naɗa shugaba don su koma bautarsu. Amma kai Allah ne mai gafartawa, mai alheri da jinƙai, mai jinkirin fushi, mai yalwar ƙauna. Saboda haka ba ka yashe su ba,
18 Lalapho sebezenzele ithole elibunjwe ngokuncibilikisa bathi: Lo nguNkulunkulu wakho, owakwenyusa eGibhithe, benza ukuhlambaza okukhulu,
ko ma sa’ad da suka yi wa kansu siffar ɗan maraƙi, suka ce, ‘Wannan shi ne allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar,’ ko sa’ad da suka yi saɓo mai bantsoro.
19 kodwa wena ngezihawu zakho ezinengi kawubatshiyanga enkangala; insika yeyezi kayisukanga kubo emini, ukubakhokhela endleleni, lensika yomlilo ebusuku, ukubakhanyisela lendlela abazahamba ngayo.
“Saboda jinƙanka mai girma, ba ka yashe su a hamada ba. Da rana, ginshiƙin girgije bai daina bishe su a hanyarsu ba, da dare kuma ginshiƙin wuta bai daina haskakawa a hanyar da za su bi ba.
20 Wabanika umoya wakho omuhle ukubafundisa, lemana yakho kawuyigodlanga emlonyeni wabo, wabanika amanzi ekomeni kwabo.
Ka ba da Ruhunka mai kyau don yă koyar da su. Ba ka janye Manna naka daga bakunansu ba, ka kuma ba su ruwa don ƙishirwansu.
21 Yebo, iminyaka engamatshumi amane wabondla enkangala, kabaswelanga lutho; izigqoko zabo kaziguganga, lenyawo zabo kazivuvukanga.
Shekaru arba’in ka riƙe su a cikin hamada; ba su rasa kome ba, rigunansu ba su yage ba, ƙafafunsu kuwa ba su kumbura ba.
22 Wasebanika imibuso lezizwe, wababela kwaze kwaba semagumbini; njalo badla ilifa lelizwe likaSihoni lelizwe lenkosi yeHeshiboni lelizwe likaOgi inkosi yeBashani.
“Ka ba su mulkoki da al’ummai, kana ba su har ma da ƙasashen da suke jeji. Suka ci ƙasar Sihon na sarkin Heshbon da ƙasar Og inda sarkin Bashan yake mulki.
23 Wandisa abantwana babo njengenkanyezi zamazulu, wabangenisa elizweni owawutshele oyise ukuthi bazangena badle ilifa lalo.
Ka sa’ya’yansu maza suka yi yawa kamar taurarin sararin sama, ka kuma kawo su cikin ƙasar da ka faɗa wa kakanninsu su shiga su mallake.
24 Sebengenile abantwana babo badla ilifa lelizwe; wehlisela phansi phambi kwabo abahlali belizwe, amaKhanani, wabanikela esandleni sabo, lamakhosi abo, labantu belizwe, ukuze benze ngabo ngokwentando yabo.
’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
25 Basebethumba imizi ebiyelweyo, lelizwe elivundileyo, badla ilifa lezindlu ezigcwele konke okuhle, imithombo egejiweyo, izivini, lezivande zemihlwathi, lezihlahla zezithelo ngobunengi. Badla-ke basutha, bazimuka, bazithokozisa ngokuhle kwakho okukhulu.
Suka kame birane masu katanga masu ƙarfi, da ƙasa masu ba da amfani; suka mallaki gidaje cike da kowane irin abu mai kyau, da rijiyoyin da aka riga aka haƙa, da gonakin inabi, da gonakin itatuwan zaitun da kuma itatuwan ba da’ya’ya a yalwace a ciki. Suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba; suka ji daɗi cikin alherinka mai girma.
26 Kube kanti kabalalelanga, bakuvukela wena, bawuphosela umlayo wakho emva komhlana wabo, babulala abaprofethi bakho abafakaza bemelene labo ukubaphendulela kuwe, benza ukuhlambaza okukhulu.
“Amma suka yi rashin biyayya suka kuma yi tawaye gare ka; suka sa dokarka a bayansu. Suka kashe annabawanka waɗanda suka gargaɗe su don su mai da su gare ka; suka aikata saɓo mai bantsoro.
27 Ngakho wabanikela esandleni sezitha zabo ezabahluphayo; kwathi ngesikhathi sokuhlupheka kwabo bakhala kuwe, wena-ke wezwa usemazulwini; langokwezisa zakho ezinengi wabanika abasindisi ababasindisa esandleni sezitha zabo.
Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
28 Kodwa sebephumulile benza okubi futhi phambi kwakho; ngakho wabatshiya esandleni sezitha zabo zaze zababusa; sebebuyile bakhala kuwe, wena wezwa usemazulwini; wabakhulula ngokwezisa zakho izikhathi ezinengi.
“Amma nan da nan, da suka sami hutu, sai suka sāke aikata abin da yake mugu a idonka. Sai ka yashe su ga hannun abokan gābansu don su yi mulki a kansu. Sa’ad da suka yi kuka kuma gare ka, ka ji daga sama, cikin jinƙanka kuma ka fisshe su sau da sau.
29 Wafakaza umelene labo ukuze ubenze babuyele emlayweni wakho; kube kanti bona baziphatha ngokuzigqaja, kabayilalelanga imilayo yakho, kodwa bemelene lezahlulelo zakho bona bemelene lazo (okuthi umuntu ezenza uzaphila ngazo), banika ihlombe lobuqholo, benza lukhuni intamo yabo, kabaze balalela.
“Ka gargaɗe su su dawo ga dokarka, amma suka yi fariya, suka bijire wa umarnanka. Suka yi zunubi game da farillanka waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu in ya yi biyayya da su. Cikin taurinkai suka juye bayansu daga gare ka, suka zama masu taurinkai, suka kuma ƙi su saurara.
30 Wababekezelela iminyaka eminengi, wafakaza umelene labo ngomoya wakho ngesandla sabaprofethi bakho, kodwa kababekanga indlebe. Ngakho wabanikela esandleni sabantu bezizwe.
Shekaru masu yawa ka yi haƙuri da su. Ta wurin Ruhunka ka gargaɗe su ta wurin annabawa. Duk da haka ba su kasa kunne ba, saboda haka ka miƙa su ga maƙwabtansu.
31 Kanti ngezisa zakho ezinengi kawubaqedanga, kawubatshiyanga; ngoba unguNkulunkulu olomusa lesihawu.
Amma cikin tausayinka mai girma ba ka kawo su ga ƙarshe ko ka yashe su ba, gama kai Allah ne mai alheri da kuma mai jinƙai.
32 Ngakho khathesi, Nkulunkulu wethu, uNkulunkulu omkhulu, olamandla lowesabekayo, ogcina isivumelwano lomusa, kakungabi kuncinyane phambi kwakho ukuhlupheka konke, okusificileyo, amakhosi ethu, iziphathamandla zethu, labapristi bethu, labaprofethi bethu, labobaba, labo bonke abantu bakho, kusukela ensukwini zamakhosi eAsiriya kuze kube lamuhla.
“To yanzu, ya Allahnmu, mai girma, mai iko, da kuma mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna, kada ka bar dukan wannan wahala ta zama kamar marar muhimmanci a idanunka, wahalar da ta zo a kanmu, a kan sarakunanmu da shugabanni, a kan firistocinmu da annabawa, a kan kakanninmu da kuma dukan mutanenka, daga kwanakin sarakunan Assuriya har yă zuwa yau.
33 Kodwa ubulungile mayelana lakho konke okusehleleyo, ngoba wenzile ngokuqonda, kodwa thina senze ngobubi.
Cikin dukan abubuwan da suka faru da mu, ka kasance mai adalci; ka yi aminci, yayinda mu kuwa muka aikata mugu.
34 Lamakhosi ethu, iziphathamandla zethu, abapristi bethu, labobaba bethu kabawenzanga umlayo wakho, kabalalelanga imithetho yakho lezifakazelo zakho owazifakaza umelene labo.
Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu da kuma kakanninmu ba su bi dokarka ba, ba su ma mai da hankali ga umarnanka ko gargaɗin da ka yi musu ba.
35 Ngoba bona kabakukhonzanga embusweni wabo lekulungeni kwakho okunengi owabanika khona lemazweni abanzi lavundileyo owawabeka phambi kwabo; njalo kabaphendukanga ezenzweni zabo ezimbi.
Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
36 Khangela, siyizigqili lamuhla, yebo, ilizwe owalinika obaba ukuthi badle isithelo salo lokuhle kwalo, khangela, siyizigqili kulo.
“Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
37 Njalo isivuno salo lisandisela amakhosi owabeke phezu kwethu ngenxa yezono zethu; njalo abusa phezu kwemizimba yethu laphezu kwezifuyo zethu ngokwentando yawo; sesisesizini olukhulu.
Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
38 Langenxa yakho konke lokhu senza isivumelwano esiqinileyo, sisibhala; iziphathamandla zethu, amaLevi ethu, abapristi bethu, basebefaka uphawu phezu kwaso.
“Saboda wannan duka, muna yin zaunannen alkawari, muna sa shi a rubuce, shugabanninmu kuwa da Lawiyawanmu, da firistocinmu suna buga hatimansu a kai.”

< UNehemiya 9 >