< UNehemiya 12 >

1 Lalaba ngabapristi lamaLevi abenyuka loZerubhabheli indodana kaSalatiyeli, loJeshuwa: OSeraya, uJeremiya, uEzra,
Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
2 uAmariya, uMaluki, uHathushi,
Amariya, Malluk, Hattush
3 uShekaniya, uRehuma, uMeremothi,
Shekaniya, Rehum, Meremot,
4 uIdo, uGinethoyi, uAbhiya,
Iddo, Ginneton, Abiya,
5 uMijamini, uMahadiya, uBiliga,
Miyamin, Mowadiya, Bilga,
6 uShemaya, loJoyaribi, uJedaya,
Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
7 uSalu, uAmoki, uHilikhiya, uJedaya. Laba babezinhloko zabapristi labafowabo ensukwini zikaJeshuwa.
Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
8 LamaLevi: OJeshuwa, uBinuwi, uKadimiyeli, uSherebiya, uJuda, uMathaniya, babephezu kokubonga, yena labafowabo.
Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
9 LoBakibukiya loUni, abafowabo, babeqondene labo emilindweni.
Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
10 UJeshuwa wasezala uJoyakimi, uJoyakimi wasezala uEliyashibi, uEliyashibi wasezala uJoyada,
Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
11 uJoyada wasezala uJonathani, uJonathani wasezala uJaduwa.
Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
12 Lensukwini zikaJoyakimi abapristi, inhloko zaboyise, babengo: OkaSeraya nguMeraya; okaJeremiya nguHananiya;
A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
13 okaEzra nguMeshulamu; okaAmariya nguJehohanani;
na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
14 okaMeliku nguJonathani; okaShebaniya nguJosefa;
na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
15 okaHarimi nguAdina; okaMerayothi nguHelikayi;
na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
16 okaIdo nguZekhariya; okaGinethoni nguMeshulamu;
na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
17 okaAbhiya nguZikiri; okaMiniyamini, okaMowadiya nguPilitayi;
na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
18 okaBiliga nguShamuwa; okaShemaya nguJehonathani;
na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
19 lokaJoyaribi nguMathenayi; okaJedaya nguUzi;
na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
20 okaSalayi nguKalayi; okaAmoki nguEberi;
na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
21 okaHilikhiya nguHashabhiya; okaJedaya nguNethaneli.
na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
22 AmaLevi ensukwini zikaEliyashibi, oJoyada loJohanani loJaduwa, babhalwa baba zinhloko zaboyise, labapristi kwaze kwaba ngumbuso kaDariyusi umPerisiya.
Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
23 Amadodana kaLevi, inhloko zaboyise, abhalwa egwalweni lwemilando, kwaze kwaba sensukwini zikaJohanani indodana kaEliyashibi.
Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
24 Lenhloko zamaLevi: OHashabhiya, uSherebiya, loJeshuwa indodana kaKadimiyeli, labafowabo maqondana labo, ukudumisa lokubonga, njengomlayo kaDavida umuntu kaNkulunkulu, umlindo maqondana lomlindo.
Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
25 OMathaniya, loBakibukiya, uObhadiya, uMeshulamu, uTalimoni, uAkubi, babengabalindimasango belinda umlindo eziphaleni zamasango.
Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
26 Labo babekhona ensukwini zikaJoyakimi indodana kaJeshuwa indodana kaJozadaki, lensukwini zikaNehemiya umbusi, loEzra umpristi, umbhali.
Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
27 Lekwehlukaniselweni komduli weJerusalema badinga amaLevi evela ezindaweni zawo zonke ukuwaletha eJerusalema ukwenza ukwehlukaniswa, langentokozo, langokubonga, langokuhlabela, ngensimbi ezincencethayo, izigubhu zezintambo, langamachacho.
A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
28 Amadodana abahlabeleli asebuthana, njalo evela emagcekeni azingelezele iJerusalema, lemizini yamaNetofa,
Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
29 leBeti-Giligali, lelizweni leGeba leAzimavethi, ngoba abahlabeleli babezakhele imizi ezingelezele iJerusalema.
daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
30 Labapristi lamaLevi bazihlambulula, bahlambulula labantu lamasango lomduli.
Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
31 Ngasengisenza iziphathamandla zakoJuda zenyukele emdulini, ngamisa amaxuku amakhulu amabili okubonga lezindwendwe, elinye kwesokunene phezu komduli kusiya esangweni lomquba.
Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
32 Lemva kwawo kwahamba oHoshaya, lengxenye yeziphathamandla zakoJuda,
Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
33 loAzariya, uEzra, loMeshulamu,
tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
34 uJuda, loBhenjamini, loShemaya, loJeremiya.
Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
35 Lakumadodana abapristi elezimpondo: OZekhariya indodana kaJonathani indodana kaShemaya indodana kaMathaniya indodana kaMikhaya indodana kaZakuri indodana kaAsafi,
da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
36 labafowabo, oShemaya, loAzareli, uMilalayi, uGilalayi, uMahayi, uNethaneli, loJuda, uHanani, belezinto zokuhlabelela zikaDavida umuntu kaNkulunkulu, loEzra umbhali ephambi kwabo.
da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
37 Langasesangweni lomthombo, njalo maqondana labo, benyuka ngezinyathelo zomuzi kaDavida, emqansweni womduli, ngaphezu kwendlu kaDavida, kusiya esangweni lamanzi ngempumalanga.
A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
38 Lexuku lesibili lokubonga lahamba maqondana lalo, lami ngililandela, lengxenye yabantu phezu komduli, kusukela ngaphezu komphotshongo wesithando kusiya emdulini obanzi,
Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
39 njalo kusukela ngaphezu kwesango lakoEfrayimi, langaphezu kwesango elidala, langaphezu kwesango lenhlanzi, lomphotshongo kaHananeli, lomphotshongo kaHameha, kusiya esangweni lezimvu; bema-ke esangweni labalindi.
bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
40 Womabili amaxuku okubonga asesima endlini kaNkulunkulu, lami, lengxenye yababusi ilami.
Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
41 Labapristi: OEliyakhimi, uMahaseya, uMiniyamini, uMikhaya, uEliyowenayi, uZekhariya, uHananiya, belezimpondo,
da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
42 loMahaseya, loShemaya, loEleyazare, loUzi, loJehohanani, loMalikiya, loElamu, loEzeri. Abahlabeleli basebezizwakalisa, loJezerahiya umboni.
haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
43 Basebehlaba mhlalokho imihlatshelo emikhulu, bathokoza, ngoba uNkulunkulu wabenza bathokoza ngentokozo enkulu; labesifazana labantwana labo bathokoza; kwaze kwathi intokozo yeJerusalema yezwakala khatshana.
A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
44 Ngalolosuku kwamiswa-ke amadoda phezu kwamakamelo okuligugu, aweminikelo, awezithelo zokuqala, lawokwetshumi, ukuqoqela kuwo okuvela emasimini emizi izabelo zomlayo zabapristi lezamaLevi. Ngoba uJuda wathokoza ngabapristi lamaLevi ayemile.
A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
45 Abahlabeleli labalindimasango basebegcina imfanelo kaNkulunkulu wabo, lemfanelo yokuhlambulula, njengomlayo kaDavida loSolomoni indodana yakhe.
Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
46 Ngoba ensukwini zamandulo zikaDavida loAsafi kwakulezinhloko zabahlabeleli lezingoma zokudumisa lokubonga kuNkulunkulu.
Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
47 LoIsrayeli wonke ensukwini zikaZerubhabheli lensukwini zikaNehemiya banika izabelo zabahlabeleli labalindimasango, udaba losuku ngosuku lwalo; basebekungcwelisela amaLevi, lamaLevi akungcwelisela abantwana bakoAroni.
Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.

< UNehemiya 12 >