< UMathewu 12 >

1 Ngalesosikhathi uJesu wadabula emasimini amabele ngesabatha; njalo abafundi bakhe babelambile, baqala ukukha izikhwebu, badla.
A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
2 Kodwa abaFarisi bekubona bathi kuye: Khangela, abafundi bakho benza okungavunyelwanga ukwenziwa ngesabatha.
Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
3 Kodwa wathi kubo: Kalifundanga yini uDavida akwenzayo, mhla elambile yena lababelaye;
Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
4 ukuthi wangena njani endlini kaNkulunkulu, wadla izinkwa zokubukiswa, ayengavunyelwa ukuzidla, ngitsho lababelaye, ngaphandle kwabapristi bodwa?
Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
5 Ingabe kalifundanga yini emlayweni, ukuthi ngamasabatha abapristi bayalona isabatha ethempelini, bangabi lacala?
Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
6 Kodwa ngithi kini: Kukhona lapha omkhulu kulethempeli.
Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
7 Kodwa aluba belisazi ukuthi kutshoni ukuthi: Ngifisa isihawu hatshi umhlatshelo, ngabe kalibalahlanga abangelacala.
Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
8 Ngoba iNdodana yomuntu iyiNkosi leyesabatha.
Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
9 Futhi wasuka lapho wangena esinagogeni labo;
Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
10 njalo khangela, kwakukhona umuntu olesandla esitshwabheneyo; basebembuza besithi: Kuvunyelwe yini ukusilisa ngamasabatha? ukuze bambeke icala.
a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
11 Kodwa wathi kubo: Nguwuphi umuntu phakathi kwenu, elemvu eyodwa, futhi uba yona iwele emgodini ngesabatha, ongayikuyibamba ayikhuphule?
Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
12 Umuntu uyedlula-ke kangakanani imvu! Ngakho kuvunyelwe ukwenza okuhle ngamasabatha.
Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
13 Wasesithi kumuntu: Yelula isandla sakho. Waseselula, sasesisiliswa saphila njengesinye.
Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
14 Basebephuma abaFarisi becebisana ngaye, ukuthi bangambulala njani.
Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
15 Kodwa uJesu esekwazi wasuka lapho; amaxuku amakhulu asemlandela, wasebasilisa bonke.
Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
16 Wasebalayisisa ukuthi bangamvezi;
yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
17 ukuze kugcwaliseke okwakhulunywa nguIsaya umprofethi, ukuthi:
Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
18 Khangela, inceku yami engiyikhethileyo; othandekayo wami othokoza ngaye umphefumulo wami; ngizabeka uMoya wami phezu kwakhe, njalo uzatshumayela ukwahlulela kwabezizwe.
“Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
19 Kayikubangisa, kayikumemeza, njalo kakho ozalizwa ilizwi lakhe ezindleleni.
Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
20 Umhlanga ofecekileyo kayikuwephula, lentambo yesibane ethunqayo kayikuyicitsha, aze aphumelelise ukwahlulela ekunqobeni.
Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
21 Lezizwe zizathemba ebizweni lakhe.
Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
22 Kwasekulethwa kuye ongenwe lidimoni, eyisiphofu lesimungulu; wasemsilisa, kwaze kwathi isiphofu esiyisimungulu sakhuluma njalo sabona.
Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
23 Asemangala amaxuku wonke athi: Lo kayisiyo yini iNdodana kaDavida?
Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
24 Kodwa abaFarisi sebezwile bathi: Lumuntu kakhuphi amadimoni, ngaphandle ngoBhelezebhule inkosi yamadimoni.
Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
25 Kodwa uJesu, eseyazi imicabango yabo, wathi kubo: Wonke umbuso owehlukene umelene lawo ngokwawo uyachitheka; lawo wonke umuzi kumbe indlu eyehlukene imelene layo ngokwayo ingeze yema.
Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
26 Njalo uba uSathane ekhupha uSathane, wehlukene emelene laye ngokwakhe; pho umbuso wakhe uzakuma njani?
In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
27 Futhi uba mina ngikhupha amadimoni ngoBhelezebhule, amadodana enu akhupha ngobani? Ngakho wona azakuba ngabagwebi benu.
In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
28 Kodwa uba mina ngikhupha amadimoni ngoMoya kaNkulunkulu, umbuso kaNkulunkulu usufikile kini.
Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
29 Kumbe umuntu angangena njani endlini yesiqhwaga aphange impahla yaso, ngaphandle kokuthi asibophe kuqala isiqhwaga? Abesephanga-ke indlu yaso.
“Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
30 Ongelami, umelene lami, longabuthi lami, uyachithiza.
“Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
31 Ngakho ngithi kini: Abantu bazathethelelwa sonke isono lokuhlambaza; kodwa ukuhlambaza uMoya kakuyikuthethelelwa abantu.
Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
32 Lalowo okhuluma ilizwi elimelana leNdodana yomuntu, uzathethelelwa; kodwa lowo okhuluma emelana loMoya oyiNgcwele, kayikuthethelelwa, kungeyisikho kulesisikhathi loba kwesizayo. (aiōn g165)
Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn g165)
33 Loba yenzani isihlahla sibe ngesilungileyo, lesithelo saso sibe ngesilungileyo, kumbe lenze isihlahla sibe sibi, lesithelo saso sibe sibi, ngoba isihlahla saziwa ngesithelo.
“Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
34 Nzalo yezinyoka, lingakhuluma njani izinto ezinhle, libabi? Ngoba umlomo ukhuluma ngokugcwala kwenhliziyo.
Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
35 Umuntu olungileyo ukhupha izinto ezilungileyo kokuligugu elilungileyo lenhliziyo; lomuntu omubi ukhupha izinto ezimbi kokuligugu elibi.
Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
36 Kodwa ngithi kini: Lonke ilizwi eliyize abalikhulumayo abantu, bazaziphendulela ngalo ngosuku lokwahlulela.
Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
37 Ngoba ngamazwi akho uzalungisiswa, langamazwi akho uzalahlwa.
Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
38 Abanye bababhali labaFarisi basebephendula, bathi: Mfundisi, sifuna ukubona isibonakaliso esivela kuwe.
Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
39 Kodwa waphendula wathi kubo: Isizukulwana esibi lesifebayo sidinga isibonakaliso; kodwa kasiyikunikwa isibonakaliso, ngaphandle kwesibonakaliso sikaJona umprofethi.
Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
40 Ngoba njengalokhu uJona waba sesiswini sensikabayitshiye insuku ezintathu lobusuku obuthathu, ngokunjalo iNdodana yomuntu izakuba semathunjini omhlaba insuku ezintathu lobusuku obuthathu.
Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
41 Amadoda eNineve azasukuma ekugwetshweni kanye lalesisizukulwana, asilahle; ngoba aphenduka ngokutshumayela kukaJona; njalo khangelani, omkhulu kuloJona ulapha.
Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
42 Indlovukazi yeningizimu izasukuma ekugwetshweni kanye lalesisizukulwana, isilahle; ngoba yavela emikhawulweni yomhlaba ukuzakuzwa inhlakanipho kaSolomoni; njalo khangelani, omkhulu kuloSolomoni ulapha.
Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
43 Kodwa nxa umoya ongcolileyo esephumile emuntwini, uyahamba adabule indawo ezomileyo, edinga ukuphumula, kodwa engakutholi.
“Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
44 Abesesithi: Ngizabuyela endlini yami engaphuma kuyo; njalo esefikile ayifice ize, ithanyelwe, njalo ilungisiwe.
Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
45 Abesehamba athathe kanye laye abanye omoya abayisikhombisa ababi kulaye uqobo, besebengena bahlale khona; njalo ukucina kwalowomuntu kube kubi kulokuqala. Kuzakuba njalo lakulesisizukulwana esibi.
Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
46 Kwathi esakhuluma emaxukwini, khangela, unina labafowabo bema ngaphandle, bedinga ukukhuluma laye.
Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
47 Omunye wasesithi kuye: Khangela, unyoko labafowenu bemi phandle, bedinga ukukhuluma lawe.
Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
48 Kodwa waphendula wathi komtshelileyo: Ngubani umama? Labafowethu ngobani?
Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
49 Waseselulela isandla sakhe kubafundi bakhe wathi: Khangelani, umama labafowethu.
Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
50 Ngoba loba ngubani owenza intando kaBaba osemazulwini, nguye ongumfowethu lodadewethu lomama.
Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”

< UMathewu 12 >