< UMakho 10 >

1 Wasesukuma lapho weza emingceleni yeJudiya edabula ngaphetsheya kweJordani; amaxuku asebuya abuthana kuye; wasephinda ukubafundisa, njengokwejwayela kwakhe.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
2 Kwasekusiza kuye abaFarisi bambuza ukuthi: Kuvunyelwe yini ukuthi indoda yale umkayo? bemlinga.
Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
3 Wasephendula wathi kubo: UMozisi walilayani?
Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 Basebesithi: UMozisi wavuma ukubhala incwadi yesehlukaniso, lokumala.
Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
5 UJesu wasephendula wathi kubo: Ngenxa yobulukhuni benhliziyo yenu walibhalela lumlayo;
Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
6 kodwa kusukela ekuqaleni kokudaliweyo, uNkulunkulu wabenza owesilisa lowesifazana.
Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
7 Ngenxa yalokhu indoda izatshiya uyise lonina, inamathele kumkayo,
‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
8 njalo labo ababili bazakuba nyamanye. Ngakho kabasebabili, kodwa banyamanye.
su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
9 Ngakho lokho uNkulunkulu akuhlanganisileyo, kakungabi lamuntu okwehlukanisayo.
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
10 Endlini abafundi bakhe basebebuya bembuza ngalokhu.
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11 Wasesithi kubo: Loba ngubani owala umkakhe athathe omunye, uyafeba kuye;
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12 lomfazi uba esala indoda yakhe endele kwenye, uyafeba.
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
13 Basebeletha abantwana abancane kuye ukuze ababambe; kodwa abafundi bakhe babakhuza ababalethayo.
Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
14 Kodwa uJesu ekubona wathukuthela, wathi kubo: Vumelani abantwana abancane beze kimi, lingabenqabeli. Ngoba umbuso kaNkulunkulu ungowabanje.
Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
15 Ngiqinisile ngithi kini: Loba ngubani ongemukeli umbuso kaNkulunkulu njengomntwana omncane, kasoze angene kuwo.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
16 Njalo ebagona, ebeka izandla zakhe phezu kwabo, wababusisa.
Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
17 Esephumele endleleni, omunye wamgijimela, eguqa phambi kwakhe wambuza wathi: Mfundisi olungileyo, ngingenzani ukuze ngidle ilifa lempilo elaphakade? (aiōnios g166)
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
18 UJesu wasesithi kuye: Ungibizelani ngokuthi olungileyo? Kakho olungileyo, ngaphandle koyedwa, uNkulunkulu.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
19 Uyayazi imilayo ethi: Ungafebi, ungabulali, ungebi, ungafakazi amanga, ungadlelezeli, hlonipha uyihlo lonyoko.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
20 Wasephendula wathi kuye: Mfundisi, lezizinto zonke ngizigcinile kusukela ebutsheni bami.
Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
21 Njalo uJesu emkhangela wamthanda, wathi kuye: Kunye okusweleyo; hamba, uthengise konke olakho, uphe abayanga, njalo uzakuba lokuligugu ezulwini; njalo uze, uthathe isiphambano, ungilandele.
Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
22 Kodwa edanile ngalelilizwi wasuka wahamba edabukile; ngoba wayelempahla ezinengi.
Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
23 UJesu wasethalaza wathi kubafundi bakhe: Kuzakuba lukhuni kangakanani kwabalenotho ukungena embusweni kaNkulunkulu.
Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
24 Abafundi basebemangala ngamazwi akhe. Kodwa uJesu ephendula futhi wathi kubo: Bantwana, kulukhuni kangakanani kwabathembela enothweni ukungena embusweni kaNkulunkulu;
Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
25 kulula ukuthi ikamela lithutshe entunjeni yenalithi, kulokuthi umuntu onothileyo angene embusweni kaNkulunkulu.
Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
26 Basebemangala kakhulukazi, bekhulumisana bathi: Pho kungasindiswa bani?
Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
27 UJesu wasebakhangela wathi: Kubantu kakulakwenzeka, kodwa kakunjalo kuNkulunkulu; ngoba zonke izinto ziyenzeka kuNkulunkulu.
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
28 UPetro waseqala ukuthi kuye: Khangela, thina sitshiye konke, sakulandela.
Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
29 UJesu wasephendula wathi: Ngiqinisile ngithi kini: Kakukho muntu otshiye indlu, kumbe abafowabo, kumbe odadewabo, kumbe uyise, kumbe unina, kumbe umkakhe, kumbe abantwana, kumbe amasimu, ngenxa yami levangeli,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
30 ongayikwemukela ngokwekhulu khathesi ngalesisikhathi, izindlu labafowabo labodadewabo labonina labantwana lamasimu, kanye lokuzingelwa, lempilo elaphakade esikhathini esizayo. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Kodwa abanengi abokuqala bazakuba ngabokucina, labokucina ngabokuqala.
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
32 Njalo babesendleleni besenyukela eJerusalema; uJesu wayesehamba phambi kwabo, njalo babemangele, belandela babesesaba. Wasethatha futhi abalitshumi lambili, waqala ukubatshela izinto ezazizakwenzakala kuye
Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
33 ukuthi: Khangelani, senyukela eJerusalema, futhi iNdodana yomuntu izanikelwa kubapristi abakhulu lakubabhali, njalo bazayigwebela ukufa, bayinikele kwabezizwe,
Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
34 bazayiyangisa, bayitshaye ngesiswepu, bayikhafulele amathe, bayibulale; njalo ngosuku lwesithathu izabuya ivuke ekufeni.
waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
35 Kwasekusiza kuye uJakobe loJohane, amadodana kaZebediya, besithi: Mfundisi, sithanda ukuthi usenzele loba yini esizayicela.
Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
36 Wasesithi kubo: Lithanda ukuthi ngilenzeleni?
Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
37 Basebesithi kuye: Siphe ukuthi sihlale omunye ngakwesokunene sakho lomunye ngakwesokhohlo sakho ebukhosini bakho.
Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
38 Kodwa uJesu wathi kubo: Kalikwazi elikucelayo. Linganatha yini inkezo engiyinathayo mina, njalo libhabhathizwe ngobhabhathizo engibhabhathizwa ngalo mina?
Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
39 Basebesithi kuye: Singakwenza. Kodwa uJesu wathi kubo: Isibili inkezo engiyinathayo mina lizayinatha; lizabhabhathizwa ngobhabhathizo engibhabhathizwa ngalo mina;
Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
40 kodwa ukuhlala ngakwesokunene sami langakwesokhohlo sami kayisikho okwami ukukupha, kodwa kungokwalabo abakulungiselweyo.
amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
41 Kwathi sebezwile abalitshumi baqala ukuthukuthela ngoJakobe loJohane.
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42 Kodwa uJesu wababizela kuye wathi kubo: Liyazi ukuthi labo okuthiwa babusa izizwe bazibusa ngobulukhuni; lezikhulu zazo zisebenzisa amandla phezu kwazo.
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43 Kodwa akuyikuba njalo phakathi kwenu; kodwa loba ngubani othanda ukuba ngomkhulu phakathi kwenu, kabe yisisebenzi senu;
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44 njalo loba ngubani othanda ukuba ngowokuqala phakathi kwenu, kabe yisisebenzi sabo bonke.
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45 Ngoba leNdodana yomuntu kayizanga ukukhonzwa, kodwa ukukhonza, lokunika impilo yayo ibe lihlawulo labanengi.
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
46 Basebefika eJeriko; kwathi esephuma eJeriko, labafundi bakhe, lexuku elikhulu, indodana kaTimewu, uBartimewu oyisiphofu wayehlezi endleleni ephanza.
Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
47 Kwathi esezwile ukuthi nguJesu weNazaretha, waqala ukumemeza lokuthi: Jesu Ndodana kaDavida, akungihawukele!
Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
48 Abanengi basebemkhuza ukuthi athule; kodwa wamemeza kakhulukazi, esithi: Ndodana kaDavida, akungihawukele!
Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
49 UJesu esima wasesithi kabizwe; basebesibiza isiphofu, besithi kuso: Mana isibindi; sukuma, uyakubiza.
Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
50 Sasesilahla isembatho saso sasukuma seza kuJesu.
Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
51 UJesu wasephendula wathi kuso: Ufuna ukuthi ngikwenzeleni? Isiphofu sasesisithi kuye: Raboni, ukuthi ngibuye ngibone.
Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
52 UJesu wasesithi kuso: Hamba; ukholo lwakho lukusindisile. Njalo sahle sabuye sabona, salandela uJesu endleleni.
Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.

< UMakho 10 >