< ULevi 25 >

1 INkosi yasikhuluma kuMozisi entabeni yeSinayi isithi:
Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai ya ce,
2 Tshono ebantwaneni bakoIsrayeli uthi kubo: Nxa lifika elizweni engilinika lona, ilizwe lizaphumula, isabatha eNkosini.
“Yi wa Isra’ilawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, dole ƙasar kanta ta kiyaye Asabbaci ga Ubangiji.
3 Iminyaka eyisithupha uzahlanyela insimu yakho, leminyaka eyisithupha uthene isivini sakho, ubuthe isithelo saso.
Shekara shida, za ku yi shuki, shekara shida kuma za ku aske gonakin inabinku, ku kuma tattara hatsinsu.
4 Kodwa ngomnyaka wesikhombisa kuzakuba lesabatha lokuphumula kwelizwe, isabatha eNkosini. Kawuyikuhlanyela insimu yakho, ungatheni isivini sakho.
Amma a shekara ta bakwai, ƙasar za tă sami hutun Asabbaci, Asabbaci ga Ubangiji. Kada ku yi shuki a gonakinku, ko kuwa ku aske gonakinku na inabi.
5 Kawuyikuvuna umkhukhuzela wesivuno sakho, kaliyikukha izithelo zamavini akho angathenwanga. Uzakuba ngumnyaka wokuphumula welizwe.
Kada ku girbe abin da ya yi girma ba tare da ku kuka shuka ba, ko ku girbe inabin da ba ku aske ba. Ƙasar za tă kasance da shekarar hutu.
6 Njalo isabatha lelizwe lizakuba yikudla kwenu, ngokwakho, lokwenceku yakho, lokwencekukazi yakho, lokoqhatshiweyo wakho, lokowemzini wakho ohlala lawe njengowezizwe,
Duk abin da gonar ta ba da amfani a shekara ta Asabbaci, zai zama abinci gare ku, wa kanku, bayinku maza da mata, da ma’aikatan da kuka ɗauka aiki, da kuma waɗanda ba zama ɗinɗinɗin suke yi tare da ku ba,
7 lokwezifuyo zakho, lokwenyamazana eziselizweni lakho; konke elikuthelayo kuzakuba yikudla.
haka ma zai zama abinci domin dabbobinku, da kuma namun jeji a ƙasarku. Duk abin da ƙasar ta bayar za a ci.
8 Uzazibalela-ke amaviki ayisikhombisa eminyaka, iminyaka eyisikhombisa ephindwe kasikhombisa, ukuze insuku zamaviki ayisikhombisa eminyaka zibe yiminyaka engamatshumi amane lesificamunwemunye kuwe.
“‘Ku ƙirga asabbatai bakwai na shekaru bakwai, sau bakwai. Gama asabbatai bakwai na shekaru bakwai za su yi daidai da shekaru arba’in da tara.
9 Khona uzadlulisa uphondo lomsindo omkhulu enyangeni yesikhombisa ngolwetshumi lwenyanga; ngosuku lwenhlawulo yokuthula lizadlulisa umsindo wophondo elizweni lonke lakini.
Sa’an nan a busa ƙaho a ko’ina, a rana ta goma ga wata na bakwai; a Ranar Kafara, a busa ƙaho a dukan ƙasarku.
10 Njalo lizangcwelisa lumnyaka wamatshumi amahlanu, limemezele inkululeko elizweni kubo bonke abakhileyo balo. Kuzakuba lijubili kini; lizabuyela, ngulowo lalowo, elifeni lakhe; futhi lizabuyela, ngulowo lalowo, kusapho lwakhe.
Ku keɓe shekara ta hamsin ku kuma yi shelar’yanci a dukan ƙasar ga mazaunanta. Za tă zama shekarar murna gare ku; kowannenku zai koma ga mallakar iyalinsa, kuma kowa ga danginsa.
11 Umnyaka wamatshumi amahlanu uzakuba ngumnyaka wejubili kini; lingahlanyeli, lingavuni umkhukhuzela wawo, lingakhi ngawo kumavini angathenwanga.
Shekara ta hamsin za tă zama ta murna a gare ku; kada ku yi shuki, kada kuma ku yi girbi abin da ya yi girma da kansa, ko ku girbe inabin da ba ku lura da shi ba.
12 Ngoba ulijubili, uzakuba ngcwele kini; lizakudla ensimini okuthelwayo kwayo.
Gama shekara ce ta murna, za tă kuma zama mai tsarki a gare ku, ku dai ci abin da aka ɗauka kai tsaye daga gonaki.
13 Ngomnyaka walelijubili lizabuyela, ngulowo lalowo elifeni lakhe.
“‘A wannan Shekara ta Murna, kowa zai koma ga mallakarsa.
14 Uba-ke uthengisa ulutho kumakhelwane wakho loba uthenga esandleni sikamakhelwane wakho, lingacindezelani.
“‘In ka sayar da gona wa wani daga mutanen ƙasarka, ko ka saya wata gona daga gare shi, kada ku cuci juna.
15 Ngokwenani leminyaka emva kwejubili uzathenga kumakhelwane wakho; ngokwenani leminyaka yokuthelwayo uzakuthengisela.
Sa’ad da mutum ya sayi fili daga abokin zamansa, kuɗin zai kasance bisa ga yawan shekara hamsin ta murna da suka wuce, da kuma bisa ga yawan shekarun noma da suka rage kafin wata shekara hamsin ta murna.
16 Ngobunengi beminyaka uzakwandisa intengo yakho; njalo ngobulutshwana beminyaka uzanciphisa intengo yakho; ngoba ekuthengisela inani lezivuno.
Idan shekarun suna da yawa, sai ku kara kuɗin filin, idan kuma shekarun ba su da yawa, sai ku rage kuɗin filin, gama ainihin abin da ake sayar maka shi ne yawan hatsin.
17 Ngakho lingacindezelani, kodwa wesabe uNkulunkulu wakho. Ngoba ngiyiNkosi uNkulunkulu wenu.
Kada ku cuci juna, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.
18 Ngakho yenzani izimiso zami, ligcine izahlulelo zami, lizenze, ukuze lihlale elizweni livikelekile.
“‘Ku bi farillaina, ku kuma yi hankali ga kiyaye dokokina, za ku kuwa zauna lafiya a ƙasar.
19 Lelizwe lizathela izithelo zalo, lidle lize lisuthe, lihlale kulo livikelekile.
Sa’an nan ƙasar za tă ba da amfaninta, za ku kuwa ci ku ƙoshi, ku kuma zauna lafiya.
20 Uba-ke lisithi: Sizakudlani ngomnyaka wesikhombisa? Khangela, kasihlanyeli, kasibuthi isivuno sethu.
Mai yiwuwa ku ce, “Me za mu ci a shekara ta bakwai in ba mu yi shuki ko girbin hatsinmu ba?”
21 Khona ngizalaya isibusiso sami kini ngomnyaka wesithupha, ukuze uthele isivuno seminyaka emithathu.
Zan aika muku da irin albarka a shekara ta shida har da ƙasar za tă ba da amfani isashe na shekara uku.
22 Njalo lizahlanyela ngomnyaka wesificaminwembili lidle okwesivuno esidala kuze kufike umnyaka wesificamunwemunye; kuze kufike isivuno sawo lizakudla esidala.
Yayinda kuke shuki a shekara ta takwas, za ku kasance da raguwa hatsi na shekarar da ta wuce, za ku kuma ci gaba da ci daga gare shi har girbin shekara ta tara yă shigo.
23 Lelizwe kaliyikuthengiswa lanininini, ngoba ilizwe ngelami; ngoba lingabemzini labahlala njengabezizwe lami.
“‘Kada a sayar da gona ɗinɗinɗin, gama ƙasar tawa ce, ku kuwa baƙi ne kawai, kuma’yan haya nawa.
24 Lelizweni lonke lelifa lenu lizavumela uhlengo lwelizwe.
Ko’ina a ƙasar da kuke da mallaka, dole ku tanadar da dama fansar ƙasar.
25 Uba umfowenu esiba ngumyanga, athengise okwelifa lakhe, uzafika umhlengi wakhe eyisihlobo sakhe, ahlenge lokho umfowabo akuthengisileyo.
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta, ya kuma sayar da mallakarsa, sai danginsa na kusa yă je yă fanshi abin da mutumin ƙasarsa ya sayar.
26 Njalo umuntu, uba engelaye umhlengi, kodwa isandla sakhe sifinyelele, athole okwenele uhlengo lwakhe,
In mutumin ba shi da wanda zai fansa masa ita, shi kansa kuwa ya wadace, ya kuma sami isashen halin fansarta,
27 kabale iminyaka yokuthengiswa kwalo, abuyisele okuseleyo kulowomuntu owamthengisela lona, abuyele elifeni lakhe.
sai yă lasafta yawan shekarun da aka yi tun da an sayar da filin. Kuɗin filin zai dangana ga yawan shekarun da suka rage kafin shekara hamsin ta murna da za tă zo; sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
28 Kodwa uba isandla sakhe singatholanga okwenele ukubuyisela kuye, okuthengisiweyo kuzakuba sesandleni sokuthengileyo kuze kufike umnyaka wejubili; kodwa ngejubili kuzaphuma, njalo uzabuyela elifeni lakhe.
Amma in bai sami halin sāke biyansa ba, abin nan da ya sayar zai ci gaba da zama mallakar mai sayan, sai Shekara ta Murna. Za a maido masa da ita a Shekara ta Murna, sa’an nan zai iya koma ga mallakarsa.
29 Umuntu, uba ethengisa-ke indlu yokuhlala emzini olomthangala, ilungelo lohlengo lwayo lizakuba kuze kuphele umnyaka wokuthengiswa kwayo; ilungelo lohlengo lwayo lizakuba ngumnyaka wonke.
“‘In mutum ya sayar da gida a birni mai katanga, yana da izini yă fanshe shi a ƙarshen shekara guda, bayan ya sayar da shi.
30 Kodwa uba ingahlengwanga uze umnyaka wayo wonke ugcwale, leyondlu esemzini olomthangala izamiselwa lowo owayithengayo njalonjalo, ezizukulwaneni zakhe; kayiyikuphuma ngejubili.
In ba a fanshe shi a ƙarshen shekara ba, gidan da yake a birni mai katanga, zai zama mallakar na ɗinɗinɗin na mai sayan da kuma zuriyarsa. Ba za a mai da shi a Shekara ta Murna ba.
31 Kodwa izindlu zemizi engabiyelwanga ngomthangala zizabalwa njengensimu yelizwe; kulohlengo lwayo, njalo izaphuma ngejubili.
Amma za a ɗauki gidaje a ƙauyuka marasa katanga kewaye da su daidai da gonaki. Za a iya fanshe su, a kuma mayar da su a Shekara ta Murna.
32 Mayelana lemizi yamaLevi, izindlu zemizi yelifa lawo, amaLevi azakuba lohlengo lwaphakade.
“‘Kullum, Lawiyawa suna da izini su fanshi gidajensu a biranen Lawiyawa waɗanda suka mallaka.
33 Uba kungohlenga kumaLevi, kuzaphuma ukuthengiswa kwendlu lokomuzi welifa lakhe ngejubili; ngoba izindlu zemizi yamaLevi ziyilifa lawo phakathi kwabantwana bakoIsrayeli.
Saboda haka ana iya fansa mallakar Lawiyawa, wato, gidan da aka sayar a duk birnin da yake nasu, za a kuma mayar a Shekara ta Murna, gama gidaje a biranen Lawiyawa, mallakar Isra’ilawa ne.
34 Kodwa insimu yamaphethelo emizi yawo kayiyikuthengiswa, ngoba iyilifa lawo kuze kube nininini.
Amma kada a sayar da filayen kiwo na waɗannan birane; mallakarsu ce, ta ɗinɗinɗin.
35 Uba-ke umfowenu esiba ngumyanga, lesandla sakhe sixega kuwe, uzamsekela: Owemzini lohlezi njengowezizwe, ukuze aphile lawe.
“‘In ɗaya daga ciki mutanen ƙasarku ya talauta, ba ya kuma iya tallafa wa kansa a cikinku, sai ku taimake shi kamar yadda za ku yi da baƙo a cikinku.
36 Ungathathi kuye umvuzo lenzuzo, kodwa wesabe uNkulunkulu wakho, ukuze umfowenu aphile lawe.
Kada ku karɓi riba ta kowace iri daga gare shi, amma ku ji tsoron Allahnku, saboda mutumin ƙasarku yă ci gaba da zama a cikinku.
37 Ungamuphi imali yakho ngenzalo, futhi ungaphi ukudla kwakho ngenzuzo.
Kada ku ba shi rancen kuɗi da ruwa, ko ku sayar masa abinci don samun riba.
38 NgiyiNkosi uNkulunkulu wenu owalikhupha elizweni leGibhithe ukulinika ilizwe leKhanani, ukuze ngibe nguNkulunkulu wenu.
Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, don in ba ku ƙasar Kan’ana in kuma zama Allahnku.
39 Uba-ke umfowenu olawe esiba ngumyanga, azithengise kuwe, ungamenzi asebenze njengesigqili;
“‘In ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku ya talauta a cikinku, ya kuma sayar da kansa gare ku, kada ku sa yă yi kamar bawa.
40 uzakuba lawe njengoqhatshiweyo, njengohlala njengowezizwe, asebenze kuwe kuze kufike umnyaka wejubili.
Amma a ɗauke shi a matsayin ma’aikacin da aka ɗauka aiki, ko mazaunan da ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, sai yă yi muku aiki sai Shekara ta Murna.
41 Khona ezaphuma kuwe, yena labantwana bakhe laye, abuyele kwabomdeni wakhe, abuyele elifeni laboyise.
Sa’an nan a sake shi da’ya’yansa, yă kuma koma ga danginsa da mallakar kakanninsa.
42 Ngoba ziyizinceku zami engazikhupha elizweni leGibhithe; kaziyikuthengiswa ngokuthengiswa kwesigqili.
Gama Isra’ilawa bayina ne, waɗanda na saya daga Masar, kada a sayar da su a matsayin bayi.
43 Ungambusi nzima, kodwa wesabe uNkulunkulu wakho.
Kada ku gwada musu azaba, amma ku ji tsoron Allahnku.
44 Lesigqili sakho lesigqilikazi sakho ozakuba lazo, zizavela ezizweni ezilizingelezeleyo; kuzo lizathenga isigqili kumbe isigqilikazi.
“‘Bayinku maza da mata, za su zo daga al’ummai da suke kewaye da ku, daga gare su za ku iya saya bayi.
45 Futhi-ke ebantwaneni balabo abahlala njengabemzini abahlala njengabezizwe lani, kubo lingazithenga lakuzizukulwana zabo ezilani, abazizalela elizweni lakini, njalo bazakuba yimfuyo yenu.
Za ku iya saya waɗansu mutanen da ba sa zama ɗinɗinɗin a cikinku, da kuma membobin danginsu da aka haifa a ƙasarku.
46 Njalo lizazenza abafuyi bazo lisenzela abantwana benu emva kwenu ukuze badle ilifa lemfuyo; lizabasebenzisa kuze kube nininini. Kodwa phakathi kwabafowenu, abantwana bakoIsrayeli, kaliyikubusa nzima, omunye phezu komunye.
Za ku iya ba da su ga’ya’yanku a matsayin kayan gādo, za ku kuma iya mai da su bayi dukan rayuwarsu, amma kada ku yi mulki a bisa’yan’uwanku Isra’ilawa da tsanani.
47 Uba-ke isandla sowezizweni loba sowemzini ohlala lawe sesifinyelele enothweni, lomfowenu olaye abe ngumyanga, azithengise kowemzini, owezizweni ohlala lawe, kumbe kusendo lwesizukulwana sowemzini,
“‘In baƙo, ko wani da yake zama ba na ɗinɗinɗin ba a cikinku, ya wadace, ɗaya daga cikin mutanen ƙasarku kuwa ya talauta, ya kuma sayar da kansa ga baƙon da yake zama a cikinku, ko memba na dangin baƙon,
48 esezithengisile kungaba lokuhlengwa kwakhe; omunye wabafowabo angamhlenga,
yana da izini samun fansa, bayan ya sayar da kansa. Ɗaya daga cikin danginsa zai iya fansarsa.
49 loba umfowabo kayise, loba umtanomfowabo kayise angamhlenga, kumbe isihlobo sakhe segazi emdeni wakhe singamhlenga; uba isandla sakhe sesifinyelele enothweni, angazihlenga.
Kawu ko yaron ɗan’uwan mahaifin wannan mutum, ko kuwa wani dangi a cikin zuriyarsa, zai iya fanshe shi. Ko kuma in ya azurta, zai iya fansar kansa.
50 Uzabalisana lowamthengayo, kusukela emnyakeni owazithengisa kuye ngawo kuze kufike umnyaka wejubili; ukuze imali yentengiso yakhe izakuba njengenani leminyaka, njengensuku zoqhatshiweyo kuzakuba njalo ngaye.
Da shi da mai sayansa, za su ƙirga lokaci daga shekarar da ya sayar da kansa har zuwa Shekara ta Murna. Farashin sakinsa zai dangana a kuɗin da ake biyan ma’aikacin da aka ɗauka aiki, na yawan shekarun ne.
51 Uba kuseleminyaka eminengi, ngokungayo uzabuyisela uhlengo lwakhe, emalini yokuthengwa kwakhe.
In shekaru sun ragu, dole yă biya don fansarsa da kuɗi mai yawa fiye da wanda aka saye shi.
52 Uba-ke kusele iminyaka emilutshwana kuze kufike umnyaka wejubili, uzabalisana laye; njengokweminyaka yakhe uzabuyisela uhlengo lwakhe.
In shekarun sun rage kaɗan ne kafin Shekara ta Murna, sai yă yi lissafin wannan, yă kuma biya fansarsa daidai wa daida.
53 Uzakuba laye njengoqhatshiweyo iminyaka ngeminyaka; kayikumbusa nzima phambi kwamehlo akho.
Sai a yi da shi kamar ma’aikacin da aka ɗauka aiki, daga shekara zuwa shekara; dole ku tabbata mai shi bai mallake shi da tsanani ba.
54 Kodwa uba engahlengwanga ngalokhu, uzaphuma ngomnyaka wejubili, yena labantwana bakhe kanye laye.
“‘Ko ma ba a fanshe shi a ɗaya daga cikin waɗannan hanyoyi ba, sai a sake shi da’ya’yansa a Shekara ta Murna,
55 Ngoba kimi abantwana bakoIsrayeli bazinceku, bazinceku zami engazikhupha elizweni leGibhithe. NgiyiNkosi uNkulunkulu wenu.
gama Isra’ilawa nawa ne a matsayin bayi. Su bayina ne waɗanda na saya daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.

< ULevi 25 >