< Izililo 5 >

1 Khumbula, Nkosi, ukuthi kwenzakaleni kithi; khangela, ubone ihlazo lethu.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Ilifa lethu seliphendulelwe kwabezizwe, izindlu zethu kwabemzini.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Siyizintandane, kungelababa; omama banjengabafelokazi.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Amanzi ethu siwanathile ngemali; inkuni zethu ziza ngentengo.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Sizingelwa ezintanyeni zethu, sidiniwe, kasilakuphumula.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Sinike isandla sethu kwabeGibhithe, labeAsiriya, ukuze sisuthiswe ngesinkwa.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Obaba bona, kabasekho, njalo thina sithwele iziphambeko zabo.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Izigqili ziyasibusa, kakho ongasihluthuna esandleni sazo.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Sizuza isinkwa sethu ngengozi yempilo yethu, ngenxa yenkemba yenkangala.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Ijwabu lethu limnyama njengeziko ngenxa yokutshisa okukhulu kwendlala.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Badlova abesifazana eZiyoni, izintombi ezimsulwa emizini yakoJuda.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Iziphathamandla zaphanyekwa ngesandla sazo; ubuso babadala kabuhlonitshwanga.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Amajaha athwala amatshe okuchola, labafana bakhubeka ngaphansi kwenkuni.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Abadala baphelile esangweni, amajaha ekuhlabeleleni.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Intokozo yenhliziyo yethu iphelile, ukugida kwethu kwaphenduka ukulila.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Umqhele wekhanda lethu uwile; hawu, maye kithi, ngoba sonile!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Ngenxa yalokhu inhliziyo yethu iphela amandla; ngenxa yalezizinto amehlo ethu afiphele.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Ngenxa yentaba yeZiyoni elunxiwa, amakhanka ahamba phezu kwayo.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Wena, Nkosi, uhlezi kuze kube nininini, isihlalo sakho sobukhosi sisuka esizukulwaneni sisiya esizukulwaneni.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Usikhohlweleni njalonjalo, usidela okobude bezinsuku?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Siphendulele kuwe, Nkosi, sizaphenduka; yenza insuku zethu zibe zintsha njengasendulo.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Kodwa ususilahlile isibili; usithukuthelele kakhulukazi.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Izililo 5 >