< UJoshuwa 3 >

1 UJoshuwa wasevuka ekuseni kakhulu, basuka eShithimi, bafika eJordani, yena labo bonke abantwana bakoIsrayeli; basebelala khona bengakachaphi.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 Kwasekusithi ekupheleni kwensuku ezintathu induna zadabula phakathi kwenkamba;
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 zalaya abantu zisithi: Nxa libona umtshokotsho wesivumelwano seNkosi uNkulunkulu wenu, labapristi, amaLevi, bewuthwele, lina-ke lisuke endaweni yenu liwulandele.
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 Kodwa kuzakuba khona ibanga phakathi kwenu lawo, phose ingalo eziyizinkulungwane ezimbili ngesilinganiso; lingasondeli kuwo; ukuze lazi indlela elizahamba ngayo, ngoba kalidlulanga ngalindlela mandulo.
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 UJoshuwa wasesithi ebantwini: Zingcweliseni, ngoba kusasa iNkosi izakwenza izimangaliso phakathi kwenu.
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 UJoshuwa wasekhuluma kubapristi esithi: Phakamisani umtshokotsho wesivumelwano, ledlule phambi kwabantu. Basebewuphakamisa umtshokotsho wesivumelwano, bahamba phambi kwabantu.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 INkosi yasisithi kuJoshuwa: Lamuhla ngizaqala ukukukhulisa emehlweni kaIsrayeli wonke ukuze bazi ukuthi njengalokho ngangiloMozisi, ngizakuba lawe.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Wena-ke uzalaya abapristi abathwele umtshokotsho wesivumelwano uthi: Nxa selifikile ekhunjini lwamanzi eJordani, lizakuma eJordani.
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 UJoshuwa wasesithi ebantwaneni bakoIsrayeli: Sondelani lapha, lizwe amazwi eNkosi uNkulunkulu wenu.
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 UJoshuwa wasesithi: Ngalokhu lizakwazi ukuthi uNkulunkulu ophilayo uphakathi kwenu, lokuthi uzawaxotsha lokuwaxotsha elifeni amaKhanani lamaHethi lamaHivi lamaPerizi lamaGirigashi lamaAmori lamaJebusi asuke ngaphambi kwenu.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Khangelani, umtshokotsho wesivumelwano seNkosi yomhlaba wonke uzachapha phambi kwenu eJordani.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Ngakho-ke zithatheleni amadoda alitshumi lambili ezizweni zakoIsrayeli, indoda ibenye kuleso lalesosizwe.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 Kuzakuthi-ke lapho ingaphansi yenyawo zabapristi abathwele umtshokotsho weNkosi, iNkosi yomhlaba wonke, zizakuma emanzini eJordani, amanzi eJordani azaqunywa, amanzi ehlayo evela phezulu; azakuma abe yinqwaba eyodwa.
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 Kwasekusithi abantu besuka emathenteni abo ukuchapha iJordani, abapristi bathwala umtshokotsho wesivumelwano phambi kwabantu.
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 Lalapho abathwele umtshokotsho befika eJordani, lenyawo zabapristi abathwele umtshokotsho zigxanyuzwa ephethelweni lamanzi (ngoba iJordani liyagcwala enkunjini zonke zalo zonke izinsuku zokuvuna),
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 amanzi ehlayo evela phezulu ema, aphakama aba yinqwaba eyodwa, khatshana kakhulu lomuzi iAdamu, oseceleni kweZarethani; lalawo ehlela elwandle lwamagceke, ulwandle lweTshwayi, aphela aqunywa. Labantu bachapha maqondana leJeriko.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 Labapristi abathwele umtshokotsho wesivumelwano seNkosi bema emhlabathini owomileyo phakathi kweJordani beqinile, loIsrayeli wonke wachapha emhlabathini owomileyo, isizwe sonke saze saqeda ukuchapha iJordani.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.

< UJoshuwa 3 >