< UJoshuwa 17 >
1 Kwasekusiba lenkatho yesizwe sakoManase, ngoba wayelizibulo likaJosefa, engekaMakiri izibulo likaManase uyise kaGileyadi; ngoba yena wayengumuntu wempi; ngakho waba leGileyadi leBashani.
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Yayikhona njalo eyabaseleyo babantwana bakoManase ngokwensendo zabo, eyabantwana bakoAbiyezeri, leyabantwana bakoHeleki, leyabantwana bakoAsiriyeli, leyabantwana bakoShekema, leyabantwana bakoHeferi, leyabantwana bakoShemida. Laba ngabantwana besilisa bakaManase indodana kaJosefa ngokwensendo zabo.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 Kodwa uZelofehadi indodana kaHeferi indodana kaGileyadi indodana kaMakiri indodana kaManase wayengelamadodana, kodwa amadodakazi. Lala ngamabizo amadodakazi akhe: OMahla loNowa, uHogila, uMilka loTiriza.
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 Asesondela phambi kukaEleyazare umpristi laphambi kukaJoshuwa indodana kaNuni laphambi kweziphathamandla, esithi: INkosi yalaya uMozisi ukusinika ilifa phakathi kwabafowethu. Ngakho wawanika ngokomlayo weNkosi ilifa phakathi kwabafowabo bakayise.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 Ngakho kwawela inkatho ezilitshumi kuManase, ngaphandle kwelizwe leGileyadi leBashani, elingaphetsheya kweJordani.
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 Ngoba amadodakazi kaManase adla ilifa phakathi kwamadodana akhe. Lelizwe leGileyadi laba ngelabaseleyo bamadodana akoManase.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 Umngcele wakoManase wasusukela eAsheri usiya eMikimethathi ephambi kweShekema; lomngcele waya ngakwesokunene kubahlali beEni-Tapuwa.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 UManase waba lelizwe leTapuwa, kodwa iTapuwa emngceleni kaManase yayingeyabantwana bakoEfrayimi.
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 Lomngcele wehlela esifuleni iKana eningizimu kwesifula. Imizi le ngeyakoEfrayimi phakathi kwemizi yakoManase. Lomngcele wakoManase usenyakatho kwesifula, lokuphuma kwawo kuselwandle.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 Eningizimu lalingelakoEfrayimi, lenyakatho lalingelakoManase, lolwandle lungumngcele wakhe. LeAsheri bahlangana enyakatho, leIsakari empumalanga.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Ngoba koIsakari loAsheri uManase wayeleBeti-Sheyani lemizana yayo, leIbileyamu lemizana yayo, labahlali beDori lemizana yayo, labahlali beEni-Dori lemizana yayo, labahlali beThahanakhi lemizana yayo, labahlali beMegido lemizana yayo: Amadundulu amathathu.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Kodwa abantwana bakoManase babengelakho ukuxotsha elifeni leyomizi, kodwa amaKhanani ayefuna ukuhlala kulelolizwe.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Kodwa kwathi lapho abantwana bakoIsrayeli sebelamandla bawasebenzisa amaKhanani njengezibhalwa, kodwa kabawaxotshanga lokuwaxotsha elifeni.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Abantwana bakoJosefa basebekhuluma kuJoshuwa besithi: Unginikeleni inkatho eyodwa lesabelo esisodwa ukuba yilifa, kube kanti ngiyisizwe esikhulu, njengoba iNkosi ingibusisile kuze kube lapha?
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 UJoshuwa wasesithi kubo: Uba uyisizwe esikhulu, wena yenyukela eguswini, uzicentele khona elizweni lamaPerizi leleziqhwaga, nxa intaba yakoEfrayimi iminyene kuwe.
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 Abantwana bakoJosefa basebesithi: Intaba kayisanelanga, njalo kulenqola zensimbi lamaKhanani wonke ahlala elizweni lesihotsha, lawaseBeti-Sheyani lemizana yayo, lawasesigodini seJizereyeli.
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 UJoshuwa wasekhuluma kundlu kaJosefa, kuEfrayimi lakuManase esithi: Uyisizwe esikhulu, futhi ulamandla amakhulu; kawuyikuba lenkatho eyodwa,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 kodwa intaba izakuba ngeyakho; ngoba iligusu, uzalicenta, lokuphuma kwalo kube ngokwakho, ngoba uzawaxotsha elifeni amaKhanani, lanxa elenqola zensimbi, lanxa elamandla.
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”