< UJohane 13 >
1 Kwathi ungakafiki umkhosi wephasika, uJesu esazi ukuthi ihola lakhe laselifikile ukuthi asuke kulumhlaba aye kuYise, esebathandile abakhe abasemhlabeni, wabathanda kwaze kwaba sekupheleni.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 Ukudla kwantambama sekwenziwe, udiyabhola esekufakile enhliziyweni kaJudasi Iskariyothi, kaSimoni, ukuthi amnikele,
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 uJesu ekwazi ukuthi uYise unikele izinto zonke ezandleni zakhe, lokuthi wavela kuNkulunkulu njalo uya kuNkulunkulu,
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 wasukuma ekudleni kwantambama, wakhupha izembatho zakhe, wathatha ilembu wazithandela ngalo.
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Emva kwalokhu wathela amanzi emganwini, waqala ukugezisa inyawo zabafundi, lokuzesula ngelembu ayezithandele ngalo.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 Wasefika kuSimoni Petro; yena wasesithi kuye: Nkosi, wena ugezisa inyawo zami yini?
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 UJesu waphendula wathi kuye: Engikwenzayo mina, kawukwazi khathesi, kodwa uzakwazi emva kwalezizinto.
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 UPetro wathi kuye: Kawusoze ugezise inyawo zami kuze kube laphakade. UJesu wamphendula wathi: Uba ngingakugezisi, kawulasabelo lami. (aiōn )
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
9 USimoni Petro wathi kuye: Nkosi, kakungabi zinyawo zami zodwa, kodwa lezandla lekhanda.
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 UJesu wathi kuye: Ogezisiweyo kasweli lutho ngaphandle kokugeziswa inyawo, kodwa uhlambulukile ngokupheleleyo; lina-ke lihlambulukile, kodwa-ke kakusini lonke.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 Ngoba wayemazi lowo owayezamnikela; ngenxa yalokhu wathi: Kalihlambulukanga lonke.
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 Esegezisile inyawo zabo, wathatha izembatho zakhe, wabuya wahlala phansi, wathi kubo: Liyakwazi yini engikwenze kini?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 Lina lingibiza lithi: Mfundisi, lokuthi Nkosi; likutsho kuhle, ngoba ngiyikho.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 Ngakho uba mina, iNkosi loMfundisi, ngigezise inyawo zenu, lani-ke lifanele ukugezisana inyawo.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 Ngoba ngilinikile isibonelo, ukuze lenze lani njengoba mina ngenzile kini.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: Inceku kayinkulu kulenkosi yayo, lothunyiweyo kamkhulu kulomthumileyo.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 Uba lisazi lezizinto, libusisiwe uba lizenza.
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 Kangikhulumi ngani lonke; mina ngiyabazi engibakhethileyo; kodwa ukuze kugcwaliseke umbhalo othi: Odla lami isinkwa ungiphakamisele isithende sakhe.
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 Sengilitshela kusukela khathesi kungakenzeki, ukuze, nxa sekusenzeka, likholwe ukuthi nginguye.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: Owemukela loba ngubani engimthumileyo, wemukela mina; lowemukela mina, wemukela ongithumileyo.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 UJesu esetshilo lezizinto wakhathazeka emoyeni, wafakaza wathi: Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini, omunye wenu uzanginikela.
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Ngakho abafundi bakhangelana, bengaqondi ukuthi ukhuluma ngobani.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 Kwakweyeme esifubeni sikaJesu omunye wabafundi bakhe, uJesu ayemthanda;
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 ngakho uSimoni Petro wamqhweba ukubuza ukuthi ngubani akhuluma ngaye.
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 Yena-ke eqamela esifubeni sikaJesu, wathi kuye: Nkosi, ngubani?
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 UJesu waphendula wathi: Ngulowo mina engizamnika ucezu sengilutshebile. Kwathi eselutshebile ucezu, walunika uJudasi Iskariyothi kaSimoni.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 Futhi emva kocezu, uSathane wasengena kuye. UJesu wasesithi kuye: Okwenzayo, kwenze masinyane.
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 Kodwa kakho kwababehlezi ekudleni owayekwazi ukuthi ukutsholoni kuye.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 Ngoba abanye bacabanga ukuthi, njengoba uJudasi wayelesikhwama, uJesu wathi kuye: Thenga esikuswelayo emkhosini; loba ukuthi kanike abayanga okunye.
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 Lowo wathi eselwemukele ucezu, wahle waphuma; kwakusebusuku.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 Ngakho kwathi esephumile, uJesu wathi: Khathesi iNdodana yomuntu idunyisiwe, loNkulunkulu udunyisiwe kuyo.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 Uba uNkulunkulu edunyiswe kuyo, loNkulunkulu uzayidumisa kuye ngokwakhe, njalo uzahle ayidumise.
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 Bantwanyana, ngiselani isikhatshana. Lizangidinga, futhi njengalokhu ngatsho kumaJuda ukuthi: Lapho mina engiya khona, lingeze leza lina; ngitsho lakini khathesi.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 Ngilinika umlayo omutsha, ukuthi lithandane; njengalokhu ngilithandile, lani-ke lithandane.
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 Ngalokhu bonke bazakwazi ukuthi lingabafundi bami, uba lilothando omunye komunye.
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 USimoni Petro wathi kuye: Nkosi, uya ngaphi? UJesu wamphendula wathi: Lapho engiya khona, ungengilandele khathesi, kodwa uzangilandela emva kwalokhu.
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 UPetro wathi kuye: Nkosi, ngingekulandele khathesi ngani? Impilo yami ngizayibekela wena phansi.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 UJesu wamphendula wathi: Impilo yakho uzayibekela mina phansi yini? Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kuwe: Iqhude kalisoze likhale uze ungiphike kathathu.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!