< UJobe 31 >

1 Ngenza isivumelwano lamehlo ami; pho ngingananzelela njani intombi?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Ngoba siyini isabelo sikaNkulunkulu esivela phezulu, lelifa likaSomandla elivela endaweni eziphezulu?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Incithakalo kayisiyomubi yini, lengozi yabenzi bobubi?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Yena kaziboni yini indlela zami, abale zonke izinyathelo zami?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Uba ngihambe ngokuyize, kumbe unyawo lwami luphuthumele enkohlisweni,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 kangilinganise ngesilinganiso esilungileyo, ukuze uNkulunkulu azi ubuqotho bami.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Uba inyathelo lami liphambukile endleleni, lenhliziyo yami yalandela amehlo ami, kumbe kunamathele isici ezandleni zami;
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 kangihlanyele, kodwa kudle omunye, lezilimo zami zisitshulwe.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Uba inhliziyo yami iyengwe ngowesifazana, kumbe ngacathama emnyango kamakhelwane wami,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 umkami kacholele omunye, labanye kabaguqe phezu kwakhe.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Ngoba lokho kuyinkohlakalo, njalo kuyisono ngabahluleli.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Ngoba ngumlilo odla kuze kube yincithakalo, usiphule sonke isivuno sami.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Uba ngalile udaba lwenceku yami loba olwencekukazi yami, lapho ziphikisana lami,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 pho ngizakwenzani lapho uNkulunkulu esukuma? Lalapho esethekela, ngizaphendulani kuye?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Lowo owangenza esiswini kamenzanga yena yini, lowasibumba esiswini munye?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Uba ngigodlele umyanga isifiso, kumbe ngifiphaze amehlo omfelokazi,
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 kumbe ngadla ucezu lwami ngedwa, ukuze intandane ingadli kulo
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 (ngoba kwasebutsheni bami yakhula lami nginjengoyise, ngamqondisa kusukela esizalweni sikamama),
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 uba ngabona obhubha ngenxa yokuswela isigqoko, loba umyanga engelasembatho,
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 uba inkalo zakhe zingangibusisanga, ngoba ekhudunyezwe yiboya bezimvu zami,
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 uba ngaphakamisa isandla sami ngimelene lentandane, lapho ngabona usizo lwami esangweni,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 kaliwe ihlombe lami esiphangeni sami, lengalo yami iqamuke ethanjeni layo.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Ngoba incithakalo kaNkulunkulu yayiyisesabiso kimi, ngingenelisi ngenxa yobukhulu bakhe.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Uba ngenzile igolide laba lithemba lami, ngathi kugolide elihle: Themba lami.
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Uba ngithokozile ngoba inotho yami inengi, langoba isandla sami sithole okunengi;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 uba ngikhangele ilanga lapho libenyezela, loba inyanga ehamba enkazimulweni,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 lenhliziyo yami yayengwa ensitha, kumbe isandla sami sange umlomo wami,
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 lalokho yisiphambeko phambi kwabehluleli, ngoba ngabe ngimphikile uNkulunkulu waphezulu.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Uba ngithokozile ngokuchitheka kongizondayo, kumbe ngajabula lapho ububi bumthola;
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 njalo ngingavumelanga umlomo wami ukuthi wone, ngokucela umphefumulo wakhe ngesiqalekiso;
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 uba abantu bethente lami bebengatshongo ukuthi: Hawu, aluba besilokwenyama yakhe, ngabe kasisuthanga.
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 Owemzini kazanga alale esitaladeni; iminyango yami ngayivulela isihambi.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Uba ngasibekela iziphambeko zami njengoAdamu, ngokufihla isono sami esifubeni sami.
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Ngoba ngethuswa lixuku elikhulu, lokudelelwa ngabensendo kwangesabisa, ngakho ngathula, kangaze ngaphuma emnyango.
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Kungathi ngabe ngilongangizwa! Khangelani uphawu lwami. Kungathi uSomandla angangiphendula, lokuthi ophikisana lami ngabe ubhale ugwalo!
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Isibili, bengingaluthwala ehlombe lami, ngilubophe lube ngumqhele kimi.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Ngimtshele inani lezinyathelo zami, ngisondele kuye njengesiphathamandla.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Uba umhlaba wami ukhalile ngami, lemifolo yawo ililile ndawonye,
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 uba ngidlile amandla awo kungelamali, kumbe ngenza umphefumulo wabaniniwo uphele,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 kakuhlume ukhula oluhlabayo endaweni yengqoloyi, lokhula olunukayo endaweni yebhali. Amazwi kaJobe asephelile.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< UJobe 31 >