< UJobe 18 >
1 Wasephendula uBilidadi umShuhi wathi:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Koze kube nini libekela amazwi imigibe? Nanzelelani, lemva kwalokho sikhulume.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Kungani sithiwa sizinyamazana, singcolile emehlweni enu?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Udwengula umphefumulo wakhe ngokuthukuthela kwakhe. Umhlaba uzatshiywa ngenxa yakho yini, loba idwala lisuswe endaweni yalo?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Yebo, ukukhanya kwabakhohlakeleyo kuzacitshwa, lenhlansi yomlilo wakhe kayiyikukhanya.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 Ukukhanya kuzafiphala ethenteni lakhe, lesibane sakhe ngaphezu kwakhe sizacitshwa.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Izinyathelo zamandla akhe zizafinyezwa, lecebo lakhe lizamwisela phansi.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Ngoba uzaphoselwa embuleni zinyawo zakhe, ahambe phezu kwembule.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Umjibila uzambamba isithende, isihitshela sizamkhulela.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Igoda lakhe lifihlwe emhlabathini, lomjibila wakhe endleleni.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Izesabiso zizamethusa inhlangothi zonke, zixotshane laye enyaweni zakhe.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Amandla akhe azaqedwa yindlala, lengozi ilindele ukukhubeka kwakhe.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Kuzakudla ingxenye zesikhumba sakhe; izibulo lokufa lidle ingxenye zakhe.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Ithemba lakhe lizahluthunwa ethenteni lakhe, njalo kumenze aye enkosini yezesabiso.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Kuzahlala ethenteni lakhe elingeyisilo lakhe; isolufa izavuvuzelwa phezu kwendawo yakhe yokuhlala.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Impande zakhe zizakoma ngaphansi, logatsha lwakhe lubune ngaphezulu.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Ukukhunjulwa kwakhe kuzabhubha emhlabeni, angabi labizo ezitaladeni.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Bazamfuqa bamsuse ekukhanyeni bamuse emnyameni, bamxotshe emhlabeni.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Kayikuba lenzalo lasizukulwana ebantwini bakibo; kakuyikuba lansali endaweni zakhe zokuhlala.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Abalandelayo bazakwethuswa lusuku lwakhe, labokuqala bazabanjwa yisesabiso.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Isibili zinjalo indawo zokuhlala zomubi, njalo yiyo le indawo yongamaziyo uNkulunkulu.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”