< UJobe 13 >
1 Khangela, konke ilihlo lami likubonile, indlebe yami izwile yakuqedisisa.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Njengokolwazi lwenu lami ngiyakwazi; kangiphansi kulani.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Kodwa mina ngizakhuluma loSomandla, ngifisa ukuqondisana loNkulunkulu.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Kodwa lina-ke ligcona ngamanga, lonke lingabelaphi abangelamsebenzi.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Kungathi ngabe liyathula lithi zwi; lokhu kube yinhlakanipho kini!
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Ake lizwe ukuzivikela kwami, lilalele impikiso zendebe zami.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Lizamkhulumela uNkulunkulu ngokubi, limkhulumele ngenkohliso yini?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Lizakwemukela ubuso bakhe, lizammela yini uNkulunkulu?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Kuzakuba kuhle yini lapho elihlola? Lizamkhohlisa yini njengokhohlisa umuntu?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Isibili uzalisola, uba lisemukela ubuso ensitha.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Ubukhulu bakhe kabulethusi yini, lokwesabeka kwakhe kulehlele?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Izikhumbuzo zenu ziyizaga zomlotha, izivikelo zenu ziyizivikelo zebumba.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Thulani lingiyekele, ukuze ngikhulume mina; kungehlele loba kuyini.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Ngizayithathelani inyama yami ngamazinyo ami, ngibeke impilo yami esandleni sami?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Lanxa ezangibulala, ngizathemba kuye. Kanti ngizazimela indlela zami phambi kwakhe.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Njalo uzakuba lusindiso lwami; ngoba umzenzisi kayikuza phambi kwakhe.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Zwisisani ilizwi lami, lengcazelo yami ngendlebe zenu.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Khangelani-ke, sengilubeke kuhle udaba lwami, ngiyazi ukuthi mina ngizalungisiswa.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Ngubani lowo ozaphikisana lami? Nxa khathesi ngithula ngizaphela.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Kuphela ungenzi izinto ezimbili kimi; khona ngingayikucatshela ubuso bakho.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Susela khatshana lami isandla sakho, lokwesabeka kwakho kungangethusi.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Ubusungibiza, mina ngizaphendula; kumbe ngikhulume, ungiphendule.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Zingaki iziphambeko lezono engilazo? Ngazisa isiphambeko sami lesono sami.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Ufihlelani ubuso bakho, ungiphathe njengesitha sakho?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Uzakwethusa yini ihlamvu eliphephethekayo? Njalo uzaxotshana lomule owomileyo yini?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Ngoba ubale izinto ezibabayo umelene lami, wangenza ngadla ilifa leziphambeko zobutsha bami.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Ufake lenyawo zami esigodweni, waqaphela zonke indlela zami, wazidweba uluphawu empandeni zezinyawo zami.
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Yena-ke njengokubolileyo uyaguga, njengesembatho inundu esidlayo.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.