< UJeremiya 10 >

1 Zwanini ilizwi iNkosi elikhuluma kini, lina ndlu kaIsrayeli.
Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
2 Itsho njalo INkosi: Lingafundi indlela yabahedeni, lingatshaywa luvalo ngezibonakaliso zamazulu, ngenxa yokuthi abahedeni bayazesaba.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
3 Ngoba imikhuba yabantu iyize; ngoba kuganyulwa isihlahla ehlathini, umsebenzi wezandla zengcitshi, ngehloka.
Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
4 Basicecisa ngesiliva langegolide, basiqinisa ngezipikili langezando, ukuze singazamazami.
Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
5 Zinjengesihlahla selala somsebenzi obaziweyo, kodwa kazikhulumi; kusweleka zithwalwe, ngoba zingehambe; lingazesabi, ngoba zingelakwenza okubi, futhi kakukho ukwenza okuhle kuzo.
Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
6 Njengoba kungekho onjengawe, Nkosi; umkhulu, lebizo lakho likhulu ngobuqhawe.
Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
7 Ngubani ongekwesabe, wena Nkosi yezizwe? ngoba kukufanele. Ngoba phakathi kwabo bonke abahlakaniphileyo bezizwe, lakuyo yonke imibuso yabo, kakho onjengawe.
Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
8 Kodwa kanyekanye banjengezinyamazana bayiziphukuphuku; isigodo siyimfundiso sokuyize.
Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
9 Isiliva esikhandiweyo silethwa sivela eTarshishi, legolide livela eUfazi, umsebenzi wengcitshi, lowezandla zomkhandi wegolide; ziluhlaza okwesibhakabhaka lokuyibubende izigqoko zabo; konke kungumsebenzi wabahlakaniphileyo.
An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
10 Kodwa iNkosi inguNkulunkulu weqiniso, inguNkulunkulu ophilayo lenkosi yaphakade. Ekuthukutheleni kwayo umhlaba uyazamazama, lezizwe kazilakulumela ulaka lwayo.
Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
11 Lizakutsho njalo kubo: Onkulunkulu abangenzanga amazulu lomhlaba bazabhubha basuke emhlabeni langaphansi kwala amazulu.
“Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
12 Owenza umhlaba ngamandla akhe, wamisa ilizwe ngenhlakanipho yakhe, langokuqedisisa kwakhe wendlala amazulu.
Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
13 Lapho ekhupha ilizwi, kulenhlokomo yamanzi emazulwini; wenza inkungu yenyuke emkhawulweni womhlaba, wenza imibane lezulu, akhuphe umoya eziphaleni zakhe.
Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
14 Wonke umuntu unjengenyamazana elwazini; wonke umkhandi wegolide uyangiswa yisithombe esibaziweyo; ngoba isithombe sakhe esibunjwe ngokuncibilikisa siyinkohliso, njalo kakulamphefumulo kuzo.
Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
15 Ziyize, umsebenzi wezinkohliso; ngesikhathi sempindiselo yazo zizabhubha.
Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
16 Isabelo sikaJakobe kasinjengazo, ngoba ungumbumbi wakho konke, loIsrayeli uyintonga yelifa lakhe; iNkosi yamabandla libizo layo.
Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
17 Qoqa impahla yakho uyikhuphe elizweni, wena mhlalikazi wenqaba.
Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
18 Ngoba itsho njalo iNkosi: Khangela, ngizabajikijela ngaphandle abahlali belizwe ngalesisikhathi, ngibacindezele ukuze bakuthole.
Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
19 Maye kimi ngenxa yokwephuka kwami! Inxeba lami linzima; kodwa mina ngathi: Isibili lokhu yinhlupheko yami engizayithwala.
Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
20 Ithente lami lidiliziwe, lentambo zami zonke ziqamukile; abantwana bami basukile kimi, njalo kabakho; kakho ongelula ithente lami futhi, amise amakhetheni ami.
An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
21 Ngoba abelusi sebenjengenyamazana, kabadinganga iNkosi; ngakho-ke kabaphumelelanga, lomhlambi wabo wonke uhlakazekile.
Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
22 Khangela, umsindo wombiko ufikile, lokuzamazama okukhulu okuvela elizweni lenyakatho, okuzakwenza imizi yakoJuda ibe lunxiwa, indawo yokuhlala yemigobho.
Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
23 Nkosi, ngiyazi ukuthi indlela yomuntu kayikho kuye; kakukho emuntwini ohambayo ukuthi aqondise ukunyathela kwakhe.
Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
24 Nkosi, ngilaya, kodwa ngesahlulelo, hatshi olakeni lwakho, hlezi unginciphise.
Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
25 Thululela ulaka lwakho phezu kwabahedeni abangakwaziyo, laphezu kwensendo ezingabizi ibizo lakho; ngoba bamdlile uJakobe, bamginya, bamqeda, bachitha indawo yakhe yokuhlala.
Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.

< UJeremiya 10 >