< U-Isaya 64 >

1 Kungathi ungadabula amazulu, wehlele phansi, izintaba zigeleze ebukhoneni bakho;
Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
2 njengokutshisa komlilo oncibilikisayo, umlilo wenze amanzi abile, ukulazisa ibizo lakho ezitheni zakho, ukuze izizwe zithuthumele ebukhoneni bakho.
Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
3 Ekwenzeni kwakho izinto ezesabekayo esasingazilindelanga, wehlela phansi; izintaba zageleza ebukhoneni bakho.
Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
4 Ngoba kusukela endulo kabezwanga, kabalalelanga ngendlebe, ilihlo kalibonanga, Nkulunkulu, ngaphandle kwakho, osebenzela lowo olindele kuye.
Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
5 Uhlangabeza othokozayo lowenza ukulunga, abakukhumbulayo ezindleleni zakho. Khangela, wena wathukuthela, ngoba sonile; kuzo kulokuqhubeka, njalo sizasindiswa.
Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
6 Kodwa sonke sinjengongcolileyo, lakho konke ukulunga kwethu kunjengezidwedwe ezingcolileyo; njalo sonke siyabuna njengehlamvu, leziphambeko zethu, njengomoya, zisiphephule.
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
7 Njalo kakho obiza ibizo lakho, ozivusela ukubambelela kuwe; ngoba ufihlile ubuso bakho kithi, wasicikiza ngenxa yeziphambeko zethu.
Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
8 Kodwa, khathesi, Nkosi, wena ungubaba wethu; thina silibumba, wena-ke ungumbumbi wethu; njalo sonke singumsebenzi wesandla sakho.
Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
9 Ungathukutheli wedlulise, Nkosi, ungakhumbuli ububi phakade. Khangela, ake ubone, sonke singabantu bakho.
Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
10 Imizi yakho engcwele isiyinkangala, iZiyoni isiyinkangala, iJerusalema iyincithakalo.
Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
11 Indlu yethu engcwele leyethu enhle, lapho obaba abakudumisela khona, itshisiwe ngomlilo; lazo zonke izinto zethu ezithandekayo sezilunxiwa.
Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
12 Uzazithinta yini ngenxa yalezizinto, Nkosi? Uzathula yini, usihluphe wedlulise?
Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?

< U-Isaya 64 >