< U-Isaya 47 >
1 Yehla, uhlale othulini, ntombi emsulwa, ndodakazi yeBhabhiloni; hlala emhlabathini; akulasihlalo sobukhosi, ndodakazi yamaKhaladiya; ngoba kawusayikubizwa ngokuthi uthambile njalo ubuthakathaka.
“Ki gangara, ki zauna a ƙura, Budurwa Diyar Babilon; ki zauna a ƙasa ba tare da rawani ba, Diyar Babiloniyawa. Ba za a ƙara kira ke marar ƙarfi’yar gata ba.
2 Thatha amatshe okuchola, uchole impuphu, wembule isimbombozo sakho, ukhwince ilogwe, uveze umlenze, uchaphe imifula.
Ɗauki dutsen niƙa ki niƙa gari; ki kware lulluɓinki. Ki ɗaga fatarinki ki bar ƙafafunki tsirara, ki kuma yi ta ratsa cikin rafuffuka.
3 Ubunqunu bakho buzakwembulwa, yebo, ihlazo lakho libonakale. Ngizaphindisela, ngingahlangani lawe njengomuntu.
Tsirararki zai bayyana za a kuma buɗe kunyarki. Zan ɗauki fansa; ba zan bar wani ba.”
4 UMhlengi wethu, iNkosi yamabandla libizo lakhe, oyiNgcwele kaIsrayeli.
Mai Fansarmu, Ubangiji Maɗaukaki shi ne sunansa, shi ne Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
5 Hlala ngokuthula, ungene emnyameni, ndodakazi yamaKhaladiya; ngoba kawusayikubizwa ngokuthi: Nkosikazi yemibuso.
“Zauna shiru, tafi cikin duhu, Diyar Babiloniya; ba za a ƙara kira ke sarauniyar masarautai.
6 Ngabathukuthelela abantu bami, ngangcolisa ilifa lami, ngabanikela esandleni sakho; kawubenzelanga izihawu; walenza laba nzima kakhulu ijogwe lakho phezu komdala.
Na yi fushi da mutanena na ƙazantar da gādona; na ba su ga hannunki, ba ki kuwa nuna musu jinƙai ba. Har ma da tsofaffi kin jibga musu kaya masu nauyi sosai.
7 Wena wathi: Ngizakuba yinkosikazi njalonjalo; kawukabeki lezizinto enhliziyweni yakho, kawukhumbulanga isiphetho sakho.
Kika ce, ‘Zan ci gaba har abada, madawwamiyar sarauniya!’ Amma ba ki lura da waɗannan abubuwa ko ki yi la’akari a kan abin da zai faru ba.
8 Khathesi-ke zwana lokhu, wena ozithokozisayo, ohlezi uvikelekile, othi enhliziyweni yakho: Yimi, njalo kakho omunye ngaphandle kwami; kangiyikuhlala okomfelokazi, kangiyikwazi ukufelwa ngabantwana.
“To, yanzu fa, ki kasa kunne, ke mai ƙaunar nishaɗi, mai zama da rai kwance kina kuma ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni. Ba zan taɓa zama gwauruwa ko in sha wahalar rashin’ya’ya ba.’
9 Kodwa lezizinto ezimbili zizakwehlela ngokucwayiza kwelihlo ngasuku lunye: Ukufelwa ngabantwana lobufelokazi; kuzakwehlela phezu kwakho ngokuphelela kwakho, ngenxa yobunengi bobuthakathi bakho, ngenxa yobunengi obukhulu bamalumbo akho.
Duk waɗannan za su sha kanki cikin farat ɗaya, a rana guda, rashin’ya’ya da gwauranci. Za su zo a kanki da cikakken minzani, duk da yawan masu dubanki da kuma dukan sihirinki.
10 Ngoba wathembela ebubini bakho, wathi: Kakho ongibonayo. Inhlakanipho yakho lolwazi lwakho khona kwakuphambula, wathi enhliziyweni yakho: Yimi, njalo kakho omunye ngaphandle kwami.
Kin dogara a muguntarki kika kuma ce, ‘Babu wanda ya gan ni.’ Hikimarki da saninki sun ɓad da ke sa’ad da kika ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni.’
11 Ngakho ububi buzakwehlela, kawusoze wazi lapho obenyuka khona; lengozi izakwehlela, ongelakho ukwenza inhlawulo yokuthula ngayo; lencithakalo ihle yehlele phezu kwakho, ungazi.
Bala’i zai fāɗo a kanki, kuma ba za ki san yadda za ki rinjaye shi yă janye ba. Masifa za tă fāɗo a kanki da ba za ki iya tsai da ita da kuɗin fansa ba; lalacewar da ba ki taɓa mafarkinta ba za tă auko miki nan da nan.
12 Mana khathesi ngamalumbo akho langobunengi bobuthakathi bakho otshikatshike kukho kusukela ebutsheni bakho; mhlawumbe uzakuba lakho ukuba lenzuzo, mhlawumbe unqobe.
“Ki dai ci gaba, da sihirinki da kuma makarunki masu yawa, waɗanda kika yi ta wahala tun kina jaririya. Mai yiwuwa ki yi nasara, mai yiwuwa ki jawo fargaba.
13 Udiniwe ebunengini bamacebo akho; kakuthi basukume khathesi abahloli bamazulu, abakhangela izinkanyezi, abazisa ngezinyanga, bakusindise kwezizakwehlela.
Dukan shawarwarin da kika samu sun dai gajiyar da ke ne kawai! Bari masananki na taurari su zo gaba, waɗannan masu zāna taswirar sammai suna kuma faɗa miki dukan abin da zai faru da ke wata-wata, bari su cece ki daga abin da zai faru da ke.
14 Khangela, bazakuba njengamabibi; umlilo uzabatshisa; kabayikuzophula emandleni elangabi; lingabikho ilahle lokotha, umlilo wokuhlala phambi kwawo.
Tabbas suna kama da bunnu; wuta za tă cinye su ƙaf. Ba za su ma iya ceton kansu daga ikon wutar ba. Ba wutar da wani zai ji ɗumi; ba wutar da za a zauna kusa da ita.
15 Bazakuba njalo kuwe labo owatshikatshika labo, owathengiselana labo kusukela ebutsheni bakho; bazazulazula, ngulowo lalowo ngendlela yakhe; kakuyikuba lomsindisi wakho.
Abin da za su iya yi miki ke nan kawai, waɗannan da kika yi ta fama da su kika kuma yi ciniki da su tun kina jaririya. Kowannensu zai tafi cikin kuskurensa; babu ko ɗayan da zai cece ki.