< U-Isaya 14 >

1 Ngoba iNkosi izamhawukela uJakobe, imkhethe futhi uIsrayeli, ibabeke elizweni lakibo; labezizwe bazahlangana labo, njalo bazanamathela endlini kaJakobe.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Labantu bazabathatha, babase endaweni yabo; lendlu kaIsrayeli izabafuya elizweni leNkosi, babe yizigqili lezigqilikazi; njalo bazathumba abathumbi babo, babuse abacindezeli babo.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Kuzakuthi-ke ngosuku iNkosi ezaliphumuza ngalo ebuhlungwini benu lekuhluphekeni kwenu lemtshikatshikeni onzima ebelisetshenziswa kiwo,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 lizaphakamisa lesisaga ngenkosi yeBhabhiloni lithi: Uphele njani umcindezeli! Owegolide usuphelile!
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 INkosi ilwephule udondolo lwabakhohlakeleyo, intonga yababusi.
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 Owatshaya abantu entukuthelweni ngokutshaya okungapheliyo, owabusa izizwe ngolaka, wazingelwa kungekho onqandayo.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Umhlaba wonke uphumule, ulokuthula; baqhamuka ngokuhlabelela.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Lezihlahla zefiri ziyathokoza ngawe, imisedari yeLebhanoni, isithi: Selokhu walala phansi, kakulamgamuli owenyukela kithi.
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Isihogo ngaphansi siyanyakaziswa ngenxa yakho ukukuhlangabeza ekuzeni kwakho; sikuvusela imimoya efileyo, impongo zonke zomhlaba, sisukumise wonke amakhosi ezizwe ezihlalweni zawo zobukhosi. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 Bonke bazaphendula bathi kuwe: Lawe usubuthakathaka njengathi; usufanana lathi.
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Ubukhosi bakho sebehliselwe esihogweni, lokukhala kwamachacho akho; izimpethu zizakwendlalwa ngaphansi kwakho, lemihlavane ikugubuzele. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 Uwe kanganani uvela emazulwini, wena okhanyayo, ndodana yokusa! Uqunyelwe emhlabathini, wena owawisela phansi izizwe!
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Wena wasusithi enhliziyweni yakho: Ngizakwenyukela emazulwini; ngaphezu kwenkanyezi zikaNkulunkulu ngiphakamise isihlalo sami sobukhosi; ngihlale entabeni yenhlangano ezinhlangothini zenyakatho;
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 ngizakwenyukela ngaphezu kwendawo eziphakemeyo zamayezi; ngizenze ngifanane loPhezukonke.
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Kodwa uzakwehliselwa esihogweni, ezinhlangothini zomgodi. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 Abakubonayo bazakujolozela, bakuqaphele, besithi: Nguye lo umuntu yini owenza ukuthi umhlaba uthuthumele, owanyakazisa imibuso,
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 owamisa ilizwe laba njengenkangala, wachitha imizi yalo, ongavulelanga izibotshwa zakhe ziye ekhaya?
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Wonke amakhosi ezizwe, wonke alala phansi ngodumo, ileyo laleyo endlini yayo;
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 kodwa wena uphoselwe ngaphandle kwengcwaba lakho, njengehlumela elinengekayo, njengelembu lababuleweyo, begwazwe ngenkemba, abehlela phansi ematsheni omgodi, njengesidumbu esinyathelelwe phansi.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Kawuyikuhlanganiswa kanye labo ekungcwatshweni, ngoba ulichithile ilizwe lakini, wabulala abantu bakini. Inzalo yabenzi bobubi kayiyikubizwa kuze kube nininini.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Lungiselani ukubulawa kwabantwana babo ngenxa yobubi baboyise, ukuze bangavuki badle ilifa lelizwe, bagcwalise ubuso bomhlaba ngemizi.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 Ngoba ngizabavukela, itsho iNkosi yamabandla, ngiqume kusuke eBhabhiloni ibizo, lensali, lendodana, lomzukulu, itsho iNkosi.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 Ngizayimisa ibe yindawo yezinhloni lamatete amanzi, ngiyithanyele ngomthanyelo wencithakalo, kutsho iNkosi yamabandla.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 INkosi yamabandla ifungile isithi: Isibili, njengokucabanga kwami kuzakuba njalo, lanjengokweluleka kwami khona kuzakuma!
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Ukuthi ngimephule umAsiriya elizweni lami, ngimnyathele phezu kwezintaba zami; beselisuka ijogwe lakhe phezu kwabo, lomthwalo wakhe usuke ehlombe labo.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Lesi yiseluleko eselulekwe ngomhlaba wonke, njalo lesi yisandla eselulelwe izizwe zonke.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Ngoba iNkosi yamabandla ikucebile, ngubani-ke ongakuphuthisa? Lesandla sayo seluliwe, njalo ngubani ongasibuyisela emuva?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 Ngomnyaka wokufa kwenkosi uAhazi kwaba lalo umthwalo:
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Ungathokozi, wena wonke Filisti, ngokuthi intonga ekutshayileyo yephukile; ngoba empandeni yenyoka kuzavela ibululu, lesithelo sabo sibe yinyoka ephaphayo etshisayo.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Lamazibulo abayanga azakwelusela, labaswelayo balale bevikelekile; kodwa ngizabulala impande yakho ngendlala, njalo abulale insali yakho.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Qhinqa isililo, sango, ukhale, muzi. Uncibilike, Filisti, wonke. Ngoba enyakatho kuvela intuthu, njalo kakho ozakuba yedwa ngezikhathi zakhe ezimisiweyo.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Lezithunywa zesizwe zizaphendulwa ngokuthini? Ngokuthi: INkosi iyisekele iZiyoni, labahluphekayo babantu bayo bazathembela kuyo.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< U-Isaya 14 >