< U-Isaya 11 >

1 Kuzavela-ke uGatsha esidindini sikaJese, leHlumela likhule empandeni zakhe.
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
2 LoMoya weNkosi uzahlala phezu kwakhe, uMoya wenhlakanipho lokuqedisisa, uMoya weseluleko lowamandla, uMoya wolwazi lowokwesaba iNkosi.
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
3 Lephunga lakhe lizakuba sekuyesabeni iNkosi; kayikwahlulela ngokubona kwamehlo akhe, njalo kayikukhuza ngokuzwa kwezindlebe zakhe;
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
4 kodwa uzakwahlulela abayanga ngokulunga, akhuze abathobekileyo bomhlaba ngobuqotho; njalo uzatshaya umhlaba ngentonga yomlomo wakhe, langomoya wendebe zakhe uzabulala okhohlakeleyo.
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
5 Njalo ukulunga kuzakuba libhanti lokhalo lwakhe, lobuqotho bube libhanti lokhalo lwakhe.
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
6 Lempisi izahlala lewundlu, njalo ingwe ilale lezinyane; lethole, lebhongo lesilwane, lokunonisiweyo ndawonye; lomfana omncinyane uzakuqhuba.
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
7 Inkomokazi lebhere kuzakudla; amathole akho alale ndawonye; lesilwane sizakudla amahlanga njengenkabi.
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
8 Lomunyayo uzadlalela phezu komlindi wenhlangwana, lolunyuliweyo afake isandla sakhe emlindini wephimpi.
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
9 Kabayikwenza okubi, njalo kabayikona entabeni yami yonke engcwele; ngoba umhlaba uzagcwala ulwazi lweNkosi njengamanzi esibekela ulwandle.
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10 Langalolosuku kuzakuba lempande kaJese ezakuma ibe luphawu ezizweni; izizwe zizadinga kuyo, lendawo yayo yokuphumula ibe lodumo.
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
11 Kuzakuthi-ke ngalolosuku iNkosi isebenzise isandla sayo futhi ngokwesibili ukubuyisa insali yabantu bayo, ezasala ivela eAsiriya leGibhithe lePatrosi leEthiyophiya leElamu leShinari leHamathi lezihlengeni zolwandle.
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
12 Izaphakamisela izizwe uphawu, ibuthe abaxotshiweyo bakoIsrayeli, iqoqe abahlakazekileyo bakoJuda, bevela ezingonsini zozine zomhlaba.
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
13 Lomhawu kaEfrayimi uzasuka, lezitha zakoJuda zizaqunywa; uEfrayimi kayikuba lomona ngoJuda, loJuda kayikucindezela uEfrayimi.
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
14 Kodwa bazaphapha phezu kwehlombe lamaFilisti ngentshonalanga; kanyekanye baphange abantwana bempumalanga; bazakwelulela isandla sabo kuEdoma loMowabi; labantwana bakoAmoni babalalele.
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
15 LeNkosi izatshabalalisa ulimi lolwandle lweGibhithe, inyikinye isandla sayo phezu komfula ngamandla omoya wayo, iwutshaye ube yizifudlana eziyisikhombisa, ibenze bachaphe ngamanyathela.
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
16 Kuzakuba khona umgwaqo omkhulu wensali yabantu bakhe abaseleyo bevela eAsiriya, njengalokhu kwakunjalo kuIsrayeli ngosuku lokwenyuka kwakhe elizweni leGibhithe.
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.

< U-Isaya 11 >