< UHoseya 13 >

1 Lapho uEfrayimi ekhuluma kwakulokuqhuqha, waziphakamisa koIsrayeli; kodwa waba lecala ngoBhali, wafa.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 Khathesi-ke baqhubeka besona, bazenzela izithombe ezibunjwe ngokuncibilikisa zesiliva sabo, izithombe njengokuqedisisa kwabo, zonke zingumsebenzi wezingcitshi; abathi ngazo: Abantu abanikela imihlatshelo bazakwanga amathole.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Ngakho bazakuba njengeyezi lekuseni, lanjengamazolo ovivi ahambayo; njengomule ophetshulwa yisivunguzane ebaleni lokubhulela, njengentuthu ephuma etshiminini.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Kube kanti mina ngiyiNkosi, uNkulunkulu wakho, kusukela elizweni leGibhithe; ngakho kawuyikwazi unkulunkulu ngaphandle kwami, ngoba kakho umsindisi ngaphandle kwami.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 Mina ngakwazi enkangala, elizweni elomileyo kakhulu.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 Njengokwedlelo labo, ngokunjalo basutha; basutha, lenhliziyo yabo yaphakama; ngenxa yalokho bangikhohlwa.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 Ngakho ngizakuba kubo njengesilwane, njengengwe endleleni ngizabacathamela.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 Ngizabahlangabeza njengebhere elithathelwe imidlwane, ngidabule isisibekelo senhliziyo yabo, ngibadlele lapho njengesilwane; isilo seganga sizabadabudabula.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Kukuchithile, Israyeli, kodwa kimi kulosizo lwakho.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Pho, ingaphi inkosi yakho, ukuthi ikusindise emizini yakho yonke? Labehluleli bakho owathi ngabo: Nginike inkosi leziphathamandla?
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 Ngakunika inkosi ekuthukutheleni kwami, ngayisusa ngolaka lwami.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 Ububi bukaEfrayimi bubotshiwe, isono sakhe sibekiwe.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 Insizi zowesifazana ohelelwayo zizamfikela; uyindodana engahlakaniphanga, ngoba ingehlale isikhathi emlonyeni wesizalo sabantwana.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 Ngizabenzela inhlawulo yokuthula emandleni engcwaba, ngibahlenge ekufeni. Kufa, bangaphi omatshayabhuqe bezifo zakho? Ngcwaba, ingaphi incithakalo yakho? Uphenduko luzasitheliswa emehlweni ami. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 Loba yena engaveza izithelo phakathi kwabafowabo, kuzafika umoya wempumalanga, umoya weNkosi, usenyuka enkangala, lomthombo wakhe uzakutsha, kome lesiphethu sakhe; wona uzaphanga okuligugu kwazo zonke izitsha eziloyisekayo.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 ISamariya izakuba lunxiwa, ngoba ihlamukele uNkulunkulu wayo; bazakuwa ngenkemba, labantwana babo bachotshozwe, labesifazana babo abakhulelweyo baqhaqhwe.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< UHoseya 13 >