< UGenesisi 8 >
1 UNkulunkulu wasemkhumbula uNowa, lakho konke okuphilayo, laso sonke isifuyo, esasilaye emkhunjini. UNkulunkulu wavunguzisa umoya phezu komhlaba, lamanzi etsha.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 Kwasekumiswa imithombo yokujula lamasango empophoma zamazulu, lezulu elivela emazulwini lanqandwa.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 Lamanzi etsha esuka emhlabeni, ehamba ebuyela; amanzi asencipha ekupheleni kwensuku ezilikhulu lamatshumi amahlanu.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 Umkhumbi wasuhlala ngenyanga yesikhombisa, ngosuku lwetshumi lesikhombisa lwenyanga, phezu kwezintaba zeArarathi.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 Lamanzi aya esetsha kwaze kwaba senyangeni yetshumi; ngeyetshumi ngosuku lokuqala lwenyanga kwabonakala ingqonga zezintaba.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 Kwasekusithi ekupheleni kwensuku ezingamatshumi amane, uNowa wasevula iwindi lomkhumbi ayelenzile,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 wasethuma iwabayi, lazulazula njalo, aze atsha amanzi emhlabeni.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 Wasethuma ijuba lisuka kuye, ukubona ukuthi amanzi asemalutshwana yini ebusweni bomhlaba;
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 kodwa ijuba kalitholanga indawo yokuphumula kwengaphansi yonyawo lwalo, ngakho labuyela kuye emkhunjini, ngoba amanzi ayekhona ebusweni bomhlaba wonke. Waseselula isandla sakhe, walithatha, walingenisa kuye emkhunjini.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 Waselinda futhi ezinye izinsuku eziyisikhombisa; wasephinda elithuma ijuba lisuka emkhunjini.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 Ijuba laselibuya kuye ngesikhathi santambama, khangela-ke, ihlamvu lomhlwathi elisanda ukuquntwa lalisemlonyeni walo; ngakho uNowa wasesazi ukuthi amanzi asemalutshwana phezu komhlaba.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 Waselinda futhi ezinye insuku eziyisikhombisa; waselithuma ijuba; kalabe lisabuyela kuye futhi.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 Kwasekusithi ngomnyaka wamakhulu ayisithupha lanye, ngenyanga yokuqala, ngolokuqala lwenyanga, amanzi atsha emhlabeni. UNowa wasesusa isifulelo somkhumbi, wabona, khangela-ke, ubuso bomhlaba babomile.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 Njalo ngenyanga yesibili, ngosuku lwamatshumi amabili lesikhombisa lwenyanga, umhlaba wawusuwomile.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 UNkulunkulu wasekhuluma kuNowa, esithi:
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 Phuma emkhunjini, wena lomkakho lamadodana akho labafazi bamadodana akho kanye lawe.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 Konke okuphilayo okulawe, kuyo yonke inyama, eyenyoni leyesifuyo leyakho konke okuhuquzelayo kuhuquzela emhlabeni, phuma lakho; ukuze kuzale kwande emhlabeni, kuzale, kwande phezu komhlaba.
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 UNowa wasephuma, lamadodana akhe, lomkakhe, labafazi bamadodana akhe kanye laye.
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 Yonke inyamazana, konke okuhuquzelayo, layo yonke inyoni, konke okuhamba emhlabeni, ngenhlobo zakho, kwaphuma emkhunjini.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 UNowa waseyakhela iNkosi ilathi; wathatha kuso sonke isifuyo esihlambulukileyo, lakuyo yonke inyoni ehlambulukileyo, wanikela umnikelo wokutshiswa phezu kwelathi.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 INkosi yasisizwa uqhatshi olumnandi; iNkosi yasisithi enhliziyweni yayo: Kangisayikuphinda ngiqalekise umhlaba ngenxa yomuntu, ngoba ukuceba kwenhliziyo yomuntu kubi kusukela ebutsheni bakhe; futhi kangisayikuphinda ngitshaye konke okuphilayo njengalokhu ngenzile.
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 Ngazo zonke izinsuku zomhlaba, ukuhlanyela lokuvuna, lamakhaza lokukhudumala, lehlobo lobusika, lemini lobusuku, kakuyikuphela.
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”