< UGenesisi 39 >
1 UJosefa wasesehliselwa eGibhithe; njalo uPotifa, umphathi kaFaro, induna yabalindi, indoda engumGibhithe, wamthenga esandleni samaIshmayeli, ababemehlisele khona.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 Njalo iNkosi yayiloJosefa, waze waba ngumuntu ophumelelayo; wayesendlini yenkosi yakhe, umGibhithe.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 Inkosi yakhe yasibona ukuthi iNkosi ilaye, lokuthi konke akwenzayo iNkosi yakuphumelelisa esandleni sakhe.
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 UJosefa wasethola umusa emehlweni ayo, wayisebenzela; njalo yamenza waba ngumphathi wendlu yayo, lakho konke eyayilakho yakunikela esandleni sakhe.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 Kwasekusithi kusukela esikhathini eyamenza ngaso umphathi wendlu yayo, lakho konke eyayilakho, iNkosi yabusisa indlu yomGibhithe ngenxa kaJosefa; lesibusiso seNkosi saba phezu kwakho konke eyayilakho, endlini lensimini.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 Yasitshiya konke eyayilakho esandleni sikaJosefa; yayingazi lutho lwayo, ngaphandle kokudla eyayikudla. Futhi uJosefa wayemuhle ngesimo, ekhangeleka kuhle.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 Kwasekusithi emva kwalezizinto, inkosikazi yenkosi yakhe yaphakamisela amehlo ayo kuJosefa; yathi: Lala lami.
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 Kodwa wala, wathi enkosikazini yenkosi yakhe: Khangela, inkosi yami kayikwazi okulami endlini, njalo konke elakho ikunikela esandleni sami;
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 kakho omkhulu kulami endlini le; njalo kayingigodlelanga lutho, ngaphandle kwakho, ngalokhu ukuthi ungumkayo; njalo ngingenza njani lobububi obukhulu, ngone kuNkulunkulu?
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 Kwasekusithi ekukhulumeni kwakhe kuJosefa insuku ngensuku, kazange amlalele, ukulala laye, lokuba laye.
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 Kwasekusithi ngosuku oluthile wangena endlini ukuyakwenza umsebenzi wakhe, njalo kwakungekho owamadoda endlu lapho endlini,
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 yasimbamba ngesembatho sakhe isithi: Lala lami. Kodwa watshiya isembatho sakhe esandleni sayo, wabaleka, waphumela phandle.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 Kwasekusithi isibonile ukuthi utshiyile isembatho sakhe esandleni sayo, wabalekela phandle,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 yabiza amadoda endlu yayo, yakhuluma kuwo isithi: Bonani, usilethele indoda engumHebheru ukudlala ngathi; uze kimi ukuze alale lami, ngamemeza ngelizwi elikhulu;
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 kwasekusithi esezwile ukuthi ngiphakamise ilizwi lami ngakhala, watshiya isembatho sakhe eceleni kwami, wabaleka, waphumela phandle.
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 Yasisibeka isembatho sakhe eceleni kwayo, yaze yafika inkosi yakhe ekhaya.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 Njalo yakhuluma kuyo njengalamazwi isithi: Inceku engumHebheru, osilethele yona, izile kimi ukuze idlale ngami;
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 kwasekusithi sengiphakamise ilizwi lami ngakhala, yatshiya isembatho sayo eceleni kwami, yabalekela phandle.
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 Kwasekusithi inkosi yakhe isizwe amazwi omkayo, ewakhulume kuyo, esithi: Njengalamazwi inceku yakho yenze kimi, ulaka lwayo lwavutha.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 Inkosi kaJosefa yasimthatha yamfaka entolongweni, indawo lapho izibotshwa zenkosi ezazibotshelwa khona; wasesiba lapho entolongweni.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 Kodwa iNkosi yaba loJosefa, yelulela umusa kuye, yasimupha umusa emehlweni enduna yentolongo.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 Induna yentolongo yanikela-ke esandleni sikaJosefa zonke izibotshwa ezazisentolongweni; lakho konke ezazikwenza lapho, wayengumenzi.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 Induna yentolongo kayisakhangelanga lutho olwalusesandleni sakhe, ngoba iNkosi yayilaye; lalokho akwenzayo iNkosi yakuphumelelisa.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.