< UGenesisi 37 >

1 UJakobe wasehlala elizweni uyise ayehlala kilo njengowezizwe, ilizwe leKhanani.
Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
2 Lezi zindaba zezizukulwana zikaJakobe. UJosefa, eleminyaka elitshumi lesikhombisa, wayeselusa umhlambi labafowabo, wayengumfana, elamadodana kaBiliha, lamadodana kaZilipa, omkayise; uJosefa waseletha kuyise imibiko emibi ngabo.
Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
3 Njalo uIsrayeli wayemthanda uJosefa kulawo wonke amadodana akhe, ngoba wayeyindodana yobudala bakhe; wamenzela isigqoko esilemibalabala.
Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
4 Kwathi abafowabo sebebonile ukuthi uyise uyamthanda kulabo bonke abafowabo, bamzonda, babengelakukhuluma kuye ngokuthula.
Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
5 UJosefa wasephupha iphupho, walazisa abafowabo; ngakho baqhubeka bemzonda kakhulu.
Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
6 Wasesithi kibo: Ake lizwe leliphupho engiliphuphileyo.
Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7 Khangelani-ke, besibopha izithungo phakathi kwensimu, njalo khangelani, isithungo sami sema saqonda futhi, khangelani-ke, izithungo zenu zazingelezela, zasikhothamela isithungo sami.
Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
8 Abafowabo basebesithi kuye: Kanti ukubusa uzasibusa, ukulawula uzasilawula yini? Ngakho baqhubeka bemzonda kakhulu, ngenxa yamaphupho akhe langenxa yamazwi akhe.
Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
9 Wasebuya futhi waphupha elinye iphupho, walilandisela abafowabo, wathi: Khangelani, ngiphuphe futhi iphupho; khangelani-ke, ilanga lenyanga lenkanyezi ezilitshumi lanye zingikhothamela.
Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
10 Waselandisela uyise labafowabo. Uyise wasemsola wathi kuye: Liyini leliphupho oliphuphileyo? Ukuza sizakuza, mina lonyoko labafowenu, sikhothamele emhlabathini phambi kwakho yini?
Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
11 Abafowabo-ke baba lomona ngaye, kodwa uyise waligcina lelilizwi.
’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
12 Abafowabo basebesiyalagisa umhlambi kayise eShekema.
To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
13 UIsrayeli wasesithi kuJosefa: Abafowenu kabalagisi eShekema yini? Woza, ngikuthume kibo. Wasesithi kuye: Khangela ngilapha.
Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
14 Wasesithi kuye: Hamba-ke, ubone ukuthi baphila kuhle yini abafowenu, lokuthi uyaphila umhlambi, ungibuyisele ilizwi. Wasemthuma esuka esigodini iHebroni wasefika eShekema.
Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
15 Indoda yamfica, ngoba khangela wayezula egangeni; indoda yasimbuza yathi: Udingani?
sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
16 Wasesithi: Ngidinga abafowethu; ake ungazise ukuthi balagise ngaphi.
Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
17 Indoda yasisithi: Basukile lapha, ngoba ngibezwile besithi: Asiye eDothani. UJosefa wasebalandela abafowabo, wabathola eDothani.
Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
18 Basebembona esekhatshana. Njalo engakasondeli kubo, bamenzela ugobe lokuthi bambulale.
Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
19 Bakhulumisana besithi: Khangela, lo umphuphi uyeza;
Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
20 khathesi-ke, wozani simbulale, simphosele komunye wemigodi, besesisithi: Isilo esibi simdlile. Khona sizabona ukuthi amaphupho akhe azakuba yini.
Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
21 URubeni wasekuzwa, wamophula esandleni sabo, wathi: Asingatshayi impilo.
Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
22 URubeni wasesithi kubo: Lingachithi igazi, mphoseleni kulumgodi osenkangala, lingeluleli isandla kuye; ukuze amkhulule esandleni sabo, ukuze ambuyisele kuyise.
Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
23 Kwasekusithi uJosefa esefikile kubafowabo, bamhlubula uJosefa isigqoko sakhe, isigqoko esilemibalabala, ayesigqokile;
Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
24 basebemthatha, bamphosela emgodini; kodwa umgodi wawungelalutho, kungelamanzi kuwo.
suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
25 Basebehlala phansi ukudla isinkwa. Baphakamisa amehlo abo babona, khangela-ke, udwendwe lwamaIshmayeli luvela eGileyadi, lamakamela awo ethwele isinongo lenhlaka lemure, ehamba ukukwehlisela eGibhithe.
Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
26 UJuda wasesithi kubafowabo: Yinzuzo bani uba simbulala umfowethu, sifihle igazi lakhe?
Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
27 Wozani, simthengise kumaIshmayeli, lesandla sethu kasingabi phezu kwakhe, ngoba umgumfowethu, inyama yethu. Abafowabo basebelalela.
Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
28 Kwasekudlula amaMidiyani angabathengiselani; basebemdonsa bamphakamisa uJosefa emgodini, bathengisa uJosefa kumaIshmayeli ngenhlamvu zesiliva ezingamatshumi amabili. Amusa-ke eGibhithe.
Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
29 Kwathi uRubeni ebuyela emgodini, khangela-ke, uJosefa wayengekho emgodini, wadabula izembatho zakhe.
Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
30 Wasebuyela kubafowabo wathi: Umfana kakho; mina-ke, ngizakuya ngaphi?
Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
31 Basebethatha isigqoko sikaJosefa, bahlaba izinyane lembuzi, bagxamuza isigqoko egazini.
Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
32 Basebethumela isigqoko esilemibalabala, basisa kuyise, bathi: Lokhu sikuficile; akunanzelele ukuthi lesi yisigqoko sendodana yakho yini, loba hatshi.
Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
33 Wasinanzelela wathi: Yisigqoko sendodana yami! Isilo esibi simdlile, isibili udatshulwe uJosefa.
Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
34 UJakobe wasedabula izembatho zakhe, wafaka isaka ekhalweni lwakhe, wayililela indodana yakhe insuku ezinengi.
Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
35 Njalo wonke amadodana akhe lamadodakazi akhe asukuma ukumduduza, kodwa wala ukududuzwa, wathi: Ngoba ngizakwehlela engcwabeni endodaneni yami ngilila. Uyise wamlilela njalo. (Sheol h7585)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
36 AmaMidiyani asemthengisa eGibhithe kuPotifa, umphathi kaFaro, induna yabalindi.
Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.

< UGenesisi 37 >