< UGenesisi 27 >

1 Kwasekusithi uIsaka esemdala lamehlo akhe esefiphele engasaboni, wabiza uEsawu indodana yakhe enkulu, wathi kuye: Ndodana yami! Wasesithi kuye: Khangela ngilapha.
Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
2 Wasesithi: Khangela-ke, sengimdala, angilwazi usuku lokufa kwami.
Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
3 Ngakho khathesi, ake uthathe izikhali zakho, isikhwama sakho semitshoko ledandili lakho, uphume uye egangeni ungizingelele inyama yenyamazana,
Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
4 ungilungisele ukudla okumnandi njengengikuthandayo, ukulethe kimi ukuthi ngidle, ukuze umphefumulo wami ukubusise ngingakafi.
Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
5 URebeka wasesizwa lapho uIsaka ekhuluma loEsawu indodana yakhe. UEsawu wasesiya egangeni ukuyazingela inyama yenyamazana ukuze ayilethe.
Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
6 URebeka wasekhuluma kuJakobe indodana yakhe, esithi: Khangela, ngizwile uyihlo ekhuluma kuEsawu umnewenu, esithi:
sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
7 Ngilethela inyama yenyamazana, ungilungisele ukudla okumnandi ukuthi ngidle, ngikubusise phambi kweNkosi ngingakafi.
‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
8 Ngakho khathesi, ndodana yami, lalela ilizwi lami kulokhu engikulaya khona.
Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
9 Ake uye emhlanjini, ungithathele lapho amazinyane amabili amahle ezimbuzi, ngizawenzela uyihlo ukudla okumnandi njengalokho akuthandayo;
Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
10 uzakusa-ke kuyihlo ukuthi adle, ukuze akubusise engakafi.
Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
11 UJakobe wasesithi kuRebeka unina: Khangela, uEsawu umnewethu uyindoda elihwanqa, kodwa ngiyindoda ebutshelezi.
Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
12 Mhlawumbe ubaba uzangiphulula, besengisiba emehlweni akhe njengomhleka usulu, njalo ngizilethele isiqalekiso kungabi-ke yisibusiso.
A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
13 Unina wasesithi kuye: Isiqalekiso sakho kasibe phezu kwami, ndodana yami; kuphela lalela ilizwi lami, uhambe ungithathele wona.
Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
14 Wasehamba, wawathatha, wawaletha kunina; unina waselungisa ukudla okumnandi njengalokho uyise akuthandayo.
Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
15 URebeka wasethatha izigqoko ezinhle zikaEsawu indodana yakhe enkulu, ayelazo endlini, wagqokisa uJakobe indodana yakhe encinyane;
Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
16 lezikhumba zamazinyane ezimbuzi wazifaka ezandleni zakhe lebutshelezini bentamo yakhe.
Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
17 Wasenika ukudla okumnandi lesinkwa ayekulungisile esandleni sikaJakobe indodana yakhe.
Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
18 Wasesiza kuyise wathi: Baba! Wasesithi: Khangela ngilapha; ungubani ndodana yami?
Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
19 UJakobe wasesithi kuyise: NginguEsawu izibulo lakho; ngenze njengoba ungitshelile; ake uvuke uhlale, udle okwenyama yami yenyamazana, ukuze umphefumulo wakho ungibusise.
Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
20 UIsaka wasesithi endodaneni yakhe: Kungani uyithole masinyane kangaka, ndodana yami? Wasesithi: Ngoba iNkosi uNkulunkulu wakho yenze ukuthi ize phambi kwami.
Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
21 UIsaka wasesithi kuJakobe: Ake usondele ukuze ngikuphulule, ndodana yami, ukuthi uyindodana yami uEsawu uqobo, kumbe hatshi.
Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
22 UJakobe wasesondela kuIsaka uyise; wasemphulula wathi: Ilizwi liyilizwi likaJakobe, kodwa izandla ziyizandla zikaEsawu.
Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
23 Kodwa kamazanga ngoba izandla zakhe zaziloboya njengezandla zomnewabo uEsawu; ngakho wambusisa.
Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
24 Wasesithi: Uyindodana yami uEsawu uqobo yini? Wasesithi: Nginguye.
Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
25 Wasesithi: Sondeza kimi ukuze ngidle okwenyama yenyamazana yendodana yami, ukuze umphefumulo wami ukubusise. Waseyisondeza kuye, wasesidla; waseletha kuye iwayini, wasenatha.
Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
26 Uyise uIsaka wasesithi kuye: Ake usondele, ungange, ndodana yami.
Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
27 Wasesondela, wamanga; wasenuka iphunga lezembatho zakhe, wambusisa wathi: Khangela, iphunga lendodana yami linjengephunga lensimu iNkosi eyibusisileyo.
Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
28 Ngakho uNkulunkulu akunike okwamazolo amazulu lokokuvunda komhlaba, lenala yamabele lewayini elitsha.
Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
29 Abantu kabakukhonze, lezizwe zikukhothamele. Bana yinkosi yabafowenu, lamadodana kanyoko akukhothamele. Okuqalekisayo kaqalekiswe, lokubusisayo kabusiswe!
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
30 Kwasekusithi uIsaka eseqedile ukubusisa uJakobe, kwathi uJakobe esanda ukuphuma phambi kukaIsaka uyise, uEsawu umnewabo wafika evela ekuzingeleni kwakhe.
Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
31 Laye futhi walungisa ukudla okumnandi, wakusa kuyise; wathi kuyise: Ubaba kavuke, adle okwenyama yenyamazana yendodana yakhe, ukuze umphefumulo wakho ungibusise.
Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
32 UIsaka uyise wasesithi kuye: Ungubani? Wasesithi: Ngiyindodana yakho, izibulo lakho uEsawu.
Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
33 UIsaka wasethuthumela ngokuthuthumela okukhulukazi, wathi: Pho, ngubani ozingele inyama yenyamazana wayiletha kimi, ngasengisidla okwayo yonke ungakafiki? Ngimbusisile, yebo uzabusiswa.
Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
34 Kwathi uEsawu esezwe amazwi kayise, wakhala ngokukhala okukhulu lokubuhlungu isibili, wathi kuyise: Ngibusisa lami njalo, baba!
Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
35 Wasesithi: Umfowenu ufike ngenkohliso, wathatha isibusiso sakho.
Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
36 Wasesithi: Kasikuthi babiza ibizo lakhe ngokuthi nguJakobe, ukuthi ungiqile lezizikhathi ezimbili? Ilungelo lobuzibulo bami ulithethe, khangela-ke, khathesi uthethe isibusiso sami. Wathi futhi: Kawungigcinelanga mina isibusiso?
Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
37 UIsaka wasephendula wathi kuEsawu: Khangela, ngimbekile abe yinkosi phezu kwakho, labo bonke abafowabo ngimnikile babe zinceku; ngimsekele ngamabele lewayini elitsha; pho, ngingabe ngisakwenzelani, ndodana yami?
Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
38 UEsawu wasesithi kuyise: Ulesibusiso esisodwa yini, baba? Ngibusisa lami njalo, baba. UEsawu waphakamisa ilizwi lakhe wakhala inyembezi.
Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
39 UIsaka uyise wasephendula wathi kuye: Khangela, umuzi wakho uzakuba khatshana lokuvunda komhlaba lakhatshana lamazolo amazulu avela phezulu.
Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
40 Njalo uzaphila ngenkemba yakho, uzakhonza umfowenu. Kodwa kuzakuthi lapho usuphunyuka, uzakwephula ijogwe lakhe entanyeni yakho.
Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
41 UEsawu wasemzonda uJakobe ngenxa yesibusiso uyise ayembusise ngaso. UEsawu wasesithi enhliziyweni yakhe: Insuku zokulilela ubaba sezisondele, khona ngizambulala umnawami uJakobe.
Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
42 Kwathi uRebeka etshelwa amazwi kaEsawu indodana yakhe enkulu, wathuma wabiza uJakobe indodana yakhe encinyane, wathi kuye: Khangela, uEsawu umnewenu uyaziduduza ngawe ukuthi akubulale.
Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
43 Ngakho khathesi, ndodana yami, lalela ilizwi lami; sukuma uzibalekele uye kuLabani umfowethu eHarani,
To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
44 njalo uhlale laye insuku ezinlutshwana, ize idede intukuthelo yomnewenu,
Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
45 kuze kuthi ulaka lomnewenu ludede kuwe, futhi akhohlwe lokho okwenze kuye; besengithuma ngikulande khona; kungani ngizalahlekelwa layini lobabili ngosuku lunye?
Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
46 URebeka wasesithi kuIsaka: Nginengekile yimpilo ngenxa yamadodakazi kaHethi; uba uJakobe ethatha umfazi kumadodakazi kaHethi anjengala, emadodakazini alelilizwe, ngiphilelani?
Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”

< UGenesisi 27 >